Home General Hukumar Custom a Najeriya ta rushe rundunarta dake da sintiri a iyakokin...

Hukumar Custom a Najeriya ta rushe rundunarta dake da sintiri a iyakokin ƙasar

Hukumar hana fasa ƙwauri ta Najeriya Custom ta rushe rundunarta ta musamman dake gudanar da sintiri a kan iyakokin ƙasar yayin da ake tsaka da zarginsu da cin zarafin jama’a.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar a Najeriya Abdullahi Maiwada a wata sanarwa da ya fitar ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan samun amincewar haka daga ofishin mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan sha’anin tsaro.

Majalisar wakilan Najeriya a ranar 11 ga watan disamba ta ɗorawa kwamitinta mai lura da hukumar kwastam ya binciki ayyukan da hukumar ke yi a iyakokin ƙasar bayan zarginsu da aka yi da taimakawa ƴan sumoga da kuma cin zarafin ƴan Najeriya.

Wannan ya biyo bayan wani ƙudirin gaggawa da ɗan majalisa Sesi Whingan ya gabatar, inda ya ce maimakon daƙile simoga jami’an kwastam a iyakokin ƙasar na bigewa da taimakawa masu fasa ƙwauri.

To sai dai mai magana da yawun hukumar hana fasa ƙwaurin ta Najeriya a sanarwar da ya fitar ya ce matakin rushe tawagar na a matsayin wani yunƙurin ofishin mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro wurin ƙarfafa tsaro a iyakokin ƙasar.

Maiwada ya ce rushe wannan tawaga ba zai kawo tsaiko ba ko kaɗan dangane da tsaron iyakokin Najeriya ko kuma kasuwanci, illa hakan wani mataki ne da zai zamanantar da ayyyukan hukumar ta Custom da ayyukanta da kuma tabbatar da tsaron Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp