Home General Hukumar Custom a Najeriya ta rushe rundunarta dake da sintiri a iyakokin...

Hukumar Custom a Najeriya ta rushe rundunarta dake da sintiri a iyakokin ƙasar

Hukumar hana fasa ƙwauri ta Najeriya Custom ta rushe rundunarta ta musamman dake gudanar da sintiri a kan iyakokin ƙasar yayin da ake tsaka da zarginsu da cin zarafin jama’a.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar a Najeriya Abdullahi Maiwada a wata sanarwa da ya fitar ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan samun amincewar haka daga ofishin mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan sha’anin tsaro.

Majalisar wakilan Najeriya a ranar 11 ga watan disamba ta ɗorawa kwamitinta mai lura da hukumar kwastam ya binciki ayyukan da hukumar ke yi a iyakokin ƙasar bayan zarginsu da aka yi da taimakawa ƴan sumoga da kuma cin zarafin ƴan Najeriya.

Wannan ya biyo bayan wani ƙudirin gaggawa da ɗan majalisa Sesi Whingan ya gabatar, inda ya ce maimakon daƙile simoga jami’an kwastam a iyakokin ƙasar na bigewa da taimakawa masu fasa ƙwauri.

To sai dai mai magana da yawun hukumar hana fasa ƙwaurin ta Najeriya a sanarwar da ya fitar ya ce matakin rushe tawagar na a matsayin wani yunƙurin ofishin mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro wurin ƙarfafa tsaro a iyakokin ƙasar.

Maiwada ya ce rushe wannan tawaga ba zai kawo tsaiko ba ko kaɗan dangane da tsaron iyakokin Najeriya ko kuma kasuwanci, illa hakan wani mataki ne da zai zamanantar da ayyyukan hukumar ta Custom da ayyukanta da kuma tabbatar da tsaron Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp