Home General Ana fargabar harin jirgin soji kan lakurawa ya hallaka mutane da dama...

Ana fargabar harin jirgin soji kan lakurawa ya hallaka mutane da dama a Sokoto

Ana fargabar al’umma da dama sun mutu wasu kuma sun jikkata sakamakon wani hari da jirgin yaƙi na soji ya kai kan Lakurawa a wasu ƙauyuka da ke Sokoton Najeriya.

Harin jirgin saman da aka kai kan ƴan ta’addan Lakurawa ya sauka kan alummar wasu ƙauyuka a ƙaramar hukumar Silame ta jihar Sokoto dake arewacin Najeriya

Kauyukan da harin ya shafa sun haɗa da Gidan Sama da Rumtuwa, kuma lamarin ya faru da misalin ƙarfe 7 na safiyar yau Laraba.

Wani mazaunin yankin Silame mai suna Malam Yahya ya ce ƙauyukan na kusa da dajin Surame inda ake zargin maboyar Lakurawa ne da ƴan bindiga.

Wata majiya ta shaidawa Dailytrust cewa sama da mutum 10 ne suka mutu kuma da dama sun jikkata a sakamakon harin jirgin saman yaƙin.

Kawo yanzu babu wata sanarwa  daga hukumomin tsaro kan lamarin.

Shugaban ƙaramar hukumar Silame Alh. Abubakar Muhammad Daftarana ya tabbatar da harin inda ya ce suna bincike kan irin barnar da harin jirgin yaƙin ya yi a ƙauyukan.

Al’ummar ƙauyukan na zaune lami lafiya lokacin da jirgin yaƙin ya yi ruwan wuta kan jama’a

Ya yi wuri na tabbatar da adadin mutanen da harin ya kashe ko suka samu raunuka saboda har yanzu muna tattara bayanai

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp