Home General Ana fargabar harin jirgin soji kan lakurawa ya hallaka mutane da dama...

Ana fargabar harin jirgin soji kan lakurawa ya hallaka mutane da dama a Sokoto

Ana fargabar al’umma da dama sun mutu wasu kuma sun jikkata sakamakon wani hari da jirgin yaƙi na soji ya kai kan Lakurawa a wasu ƙauyuka da ke Sokoton Najeriya.

Harin jirgin saman da aka kai kan ƴan ta’addan Lakurawa ya sauka kan alummar wasu ƙauyuka a ƙaramar hukumar Silame ta jihar Sokoto dake arewacin Najeriya

Kauyukan da harin ya shafa sun haɗa da Gidan Sama da Rumtuwa, kuma lamarin ya faru da misalin ƙarfe 7 na safiyar yau Laraba.

Wani mazaunin yankin Silame mai suna Malam Yahya ya ce ƙauyukan na kusa da dajin Surame inda ake zargin maboyar Lakurawa ne da ƴan bindiga.

Wata majiya ta shaidawa Dailytrust cewa sama da mutum 10 ne suka mutu kuma da dama sun jikkata a sakamakon harin jirgin saman yaƙin.

Kawo yanzu babu wata sanarwa  daga hukumomin tsaro kan lamarin.

Shugaban ƙaramar hukumar Silame Alh. Abubakar Muhammad Daftarana ya tabbatar da harin inda ya ce suna bincike kan irin barnar da harin jirgin yaƙin ya yi a ƙauyukan.

Al’ummar ƙauyukan na zaune lami lafiya lokacin da jirgin yaƙin ya yi ruwan wuta kan jama’a

Ya yi wuri na tabbatar da adadin mutanen da harin ya kashe ko suka samu raunuka saboda har yanzu muna tattara bayanai

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp