Home General Rundunar sojin Najeriya ta ƙaryata kai harin kuskure kan fararen hula a...

Rundunar sojin Najeriya ta ƙaryata kai harin kuskure kan fararen hula a Sokoto

Rundunar sojojin haɗin gwiwa ta Najeriya ta Operation Fansan Yamma, ta buƙuci jama’a su rinƙa dogara da ingantattun bayanai don hana yaɗa rahotannin ƙarya da ke haifar da shakku game da ayyukanta.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na rundunar Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, wacce ke mai da martani game da rahotannin da ke cewar wani jirgin yaƙin sojin Najeriya ya kai harin bam wasu kauyuka a ƙaramar hukumar Silame da ke jihar Sakoto, inda ake fargabar mutane da dama sun rasa ransu.

Rundunar ta ce sai da ta tabbatar da cewar inda ta kai harin a garuwan Gidan Sama da kuma Rumtuwa, suna da alaƙa da ƙungiyar ƴan ta’adda ta Lakurawa.

Laftanar Kanar Abdullahi ya ce rundunar na gudanar da dukkan ayyukanta ne bayan tattara bayanan siri da kuma bincike.

Wasu majiyoyi sun ruwaito cewa mutane 10 ne suka rasu yayin hare-haren, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Shugaban Ƙaramar Hukumar ta Silame, Alhaji Abubakar Muhammad Daftarana, ya tabbatar da faruwar harin, sai dai ya ce har yanzu suna aikin tantance irin ɓarnar da harin ya yi.

Tuni dai gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya ziyarci kauyukan da abin ya faru don jajantawa iyalan waɗanda ibtila’in ya shafa, tare da yin alkawarin kafa kwamiti don gudanar da bincike akai.

Na kaɗu matuka da faruwan wannan lamarin, ba da gangan jami’an tsaro suka yi ba, haƙiƙa sun je kai wa ƴan ta’addan hari ne, sun yi nasarar kashe ƴan ta’adda a hari na farko da na biyu, sai dai an samu kuskure a na uku.

Wannan dai ba shi ne karo na farko ba da ake samun hare-heren kuskure kan fararen hula a Najeriya, wanda kuma ke haifar da asarar dimbin rayukan al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp