Home General Rundunar sojin Najeriya ta ƙaryata kai harin kuskure kan fararen hula a...

Rundunar sojin Najeriya ta ƙaryata kai harin kuskure kan fararen hula a Sokoto

Rundunar sojojin haɗin gwiwa ta Najeriya ta Operation Fansan Yamma, ta buƙuci jama’a su rinƙa dogara da ingantattun bayanai don hana yaɗa rahotannin ƙarya da ke haifar da shakku game da ayyukanta.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na rundunar Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, wacce ke mai da martani game da rahotannin da ke cewar wani jirgin yaƙin sojin Najeriya ya kai harin bam wasu kauyuka a ƙaramar hukumar Silame da ke jihar Sakoto, inda ake fargabar mutane da dama sun rasa ransu.

Rundunar ta ce sai da ta tabbatar da cewar inda ta kai harin a garuwan Gidan Sama da kuma Rumtuwa, suna da alaƙa da ƙungiyar ƴan ta’adda ta Lakurawa.

Laftanar Kanar Abdullahi ya ce rundunar na gudanar da dukkan ayyukanta ne bayan tattara bayanan siri da kuma bincike.

Wasu majiyoyi sun ruwaito cewa mutane 10 ne suka rasu yayin hare-haren, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Shugaban Ƙaramar Hukumar ta Silame, Alhaji Abubakar Muhammad Daftarana, ya tabbatar da faruwar harin, sai dai ya ce har yanzu suna aikin tantance irin ɓarnar da harin ya yi.

Tuni dai gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya ziyarci kauyukan da abin ya faru don jajantawa iyalan waɗanda ibtila’in ya shafa, tare da yin alkawarin kafa kwamiti don gudanar da bincike akai.

Na kaɗu matuka da faruwan wannan lamarin, ba da gangan jami’an tsaro suka yi ba, haƙiƙa sun je kai wa ƴan ta’addan hari ne, sun yi nasarar kashe ƴan ta’adda a hari na farko da na biyu, sai dai an samu kuskure a na uku.

Wannan dai ba shi ne karo na farko ba da ake samun hare-heren kuskure kan fararen hula a Najeriya, wanda kuma ke haifar da asarar dimbin rayukan al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp