Home General Rundunar sojin Najeriya ta ƙaryata kai harin kuskure kan fararen hula a...

Rundunar sojin Najeriya ta ƙaryata kai harin kuskure kan fararen hula a Sokoto

Rundunar sojojin haɗin gwiwa ta Najeriya ta Operation Fansan Yamma, ta buƙuci jama’a su rinƙa dogara da ingantattun bayanai don hana yaɗa rahotannin ƙarya da ke haifar da shakku game da ayyukanta.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na rundunar Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, wacce ke mai da martani game da rahotannin da ke cewar wani jirgin yaƙin sojin Najeriya ya kai harin bam wasu kauyuka a ƙaramar hukumar Silame da ke jihar Sakoto, inda ake fargabar mutane da dama sun rasa ransu.

Rundunar ta ce sai da ta tabbatar da cewar inda ta kai harin a garuwan Gidan Sama da kuma Rumtuwa, suna da alaƙa da ƙungiyar ƴan ta’adda ta Lakurawa.

Laftanar Kanar Abdullahi ya ce rundunar na gudanar da dukkan ayyukanta ne bayan tattara bayanan siri da kuma bincike.

Wasu majiyoyi sun ruwaito cewa mutane 10 ne suka rasu yayin hare-haren, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Shugaban Ƙaramar Hukumar ta Silame, Alhaji Abubakar Muhammad Daftarana, ya tabbatar da faruwar harin, sai dai ya ce har yanzu suna aikin tantance irin ɓarnar da harin ya yi.

Tuni dai gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya ziyarci kauyukan da abin ya faru don jajantawa iyalan waɗanda ibtila’in ya shafa, tare da yin alkawarin kafa kwamiti don gudanar da bincike akai.

Na kaɗu matuka da faruwan wannan lamarin, ba da gangan jami’an tsaro suka yi ba, haƙiƙa sun je kai wa ƴan ta’addan hari ne, sun yi nasarar kashe ƴan ta’adda a hari na farko da na biyu, sai dai an samu kuskure a na uku.

Wannan dai ba shi ne karo na farko ba da ake samun hare-heren kuskure kan fararen hula a Najeriya, wanda kuma ke haifar da asarar dimbin rayukan al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp