Home General Sokoto: Babu hujjar kashe mutanen da babu ruwansu – Atiku

Sokoto: Babu hujjar kashe mutanen da babu ruwansu – Atiku

Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya ce babu wata hujjar da za a bayar kan kashe mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.

Atiku ya bayyana haka a saƙonsa na jaje game da ibtila’in da ya auku a jihar Sokoto, inda hare-haren sojoji ‘bisa kuskure’ ya yi ajalin aƙalla mutum 10, ya jikkata wasu.

Atiku ya ce yadda kuskuren ke maimiatuwa ya sa ake tambayar wane darasi aka ɗauka a baya.

A cewarsa, “A ranar 3 ga Disamban 2023, gomman mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba ne suka rasu a Tudun Biri da ke Kaduna. Shin mutum nawa za su ƙara mutuwa kafin a ɗauki mataki? Duk da cewa yana da kyau a ƙaddamar da hare-hare kan ƴanbindiga, amma ai akwai buƙatar a yi amfani da ƙwarewa.”

“Babu wata hujjar da za a bayar kan kashe mutanen da babu ruwansu. Irin haka na nuna rashin ƙwarewa da tauye haƙƙin ɗan’adam.”

Ya ce hakan zai sa mutane su kasa bambance masu kare su da waɗanda suka kashe, inda ya ce dole a kawo ƙarshen irin wannan kashe-kashen bisa kuskure.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp