Home General Sokoto: Babu hujjar kashe mutanen da babu ruwansu – Atiku

Sokoto: Babu hujjar kashe mutanen da babu ruwansu – Atiku

Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya ce babu wata hujjar da za a bayar kan kashe mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.

Atiku ya bayyana haka a saƙonsa na jaje game da ibtila’in da ya auku a jihar Sokoto, inda hare-haren sojoji ‘bisa kuskure’ ya yi ajalin aƙalla mutum 10, ya jikkata wasu.

Atiku ya ce yadda kuskuren ke maimiatuwa ya sa ake tambayar wane darasi aka ɗauka a baya.

A cewarsa, “A ranar 3 ga Disamban 2023, gomman mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba ne suka rasu a Tudun Biri da ke Kaduna. Shin mutum nawa za su ƙara mutuwa kafin a ɗauki mataki? Duk da cewa yana da kyau a ƙaddamar da hare-hare kan ƴanbindiga, amma ai akwai buƙatar a yi amfani da ƙwarewa.”

“Babu wata hujjar da za a bayar kan kashe mutanen da babu ruwansu. Irin haka na nuna rashin ƙwarewa da tauye haƙƙin ɗan’adam.”

Ya ce hakan zai sa mutane su kasa bambance masu kare su da waɗanda suka kashe, inda ya ce dole a kawo ƙarshen irin wannan kashe-kashen bisa kuskure.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp