Home General Gwamnatin Najeriya ta ƙaryata zarge-zargen shugaban mulkin sojin Nijar

Gwamnatin Najeriya ta ƙaryata zarge-zargen shugaban mulkin sojin Nijar

Gwamnatin Najeriya ta ce zargin da shugaban mulkin Sojin Nijar Abdourahmane Tchiani ya yi cewa ƙasar na ƙoƙarin haɗa kai da Faransa wurin kawo hargitsi ba shi da tushe ballantana makama.

Ministan yaɗa labarai na Najeriya Mohammed Idris ne ya bayyana haka a wata takadda da ya fitar a yammacin yau a matsayin martani kan wata hira da shugaban mulkin soji na Jamhuriyar Nijar Tchiani ya yi. inda ya zargi Najeriya da ƙoƙarin kawowa ƙasar tsaiko.

Sanarwar ta ce shugaban Najeriya Bola Tinubu a mtsayinsa na shugaban ƙungiyar raya tattalin arzikin kasashen Afrika ta yamma ECOWAS ya nuna shugabanci abin koyi tare da barin ƙofa a buɗe ga Jamhuriyar Nijar duk kuwa da halin da ake ciki na juyin mulki a ƙasar.

Najeriya ta ce a shirye take wurin tabbatar da kyakykyawar alaƙa da zaman lafiya da fahimtar juna da kuma kyautata alaƙar diflomasiyya mai tsohon tarihi dake tsakaninta da Nijar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa dakarun sojin Najeriya haɗin gwiwa da abokanan hulɗarta na samun nasara sosai wurin yaƙi da ta’addanci a yankin, don haka abin mamaki ne ace ƙasar za ta haɗa kai da wata ƙasar waje wurin kawo tsaiko ko rashin zaman lafiya a makwaftan ƙasashe.

Gwamnatin Najeriyar ta ce babu wani jami’inta da ya taɓa goyan bayan ƙungiyoyin ƴan ta’adda ko wata kungiyar ƴan ta’adda wurin kaiwa Nijar hari.

Gwamnatin ƙasar ta ce Najeriya ta tsaye kan kafafunta da cikakken iko kan ƙasar. kuma ba ta taɓa bai wa wata ƙasa dama ko iko na kafa sansanin soji a cikinta ba, sabanin abin da wasu ƙasashe ke yi. Wannan na nuna yadda shugabancin Najeriya ya yi tsayuwar daka wurin tabbatar da  ƴancin ƙasar.

Dangane da zargin da shugaban ƙasar Nijar ya yi cewa ana shirin kawowa bututun mansu da ayyukan gona tazgaro  gwamnatin ta ce kwata-kwata ba gaskiya bane.

Gwamnatin Najeriya ta ce waɗannan zarge-zarge da shugaban mulkin sojin Nijar Abdourahmane Tchiani ya yi tamkar kawar da hankalin jama’a ne kan gazawar da mulkinsa ya yi tun bayan da ya jagoranci juyin mulki. inda gwamnatin ta buƙaci da Jamhuriyar Nijar ta mayar da hankali wurin tattaunawa da haɗa kai maimakon zarge-zarge marasa tushe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp