Home General Gwamnatin Najeriya ta ƙaryata zarge-zargen shugaban mulkin sojin Nijar

Gwamnatin Najeriya ta ƙaryata zarge-zargen shugaban mulkin sojin Nijar

Gwamnatin Najeriya ta ce zargin da shugaban mulkin Sojin Nijar Abdourahmane Tchiani ya yi cewa ƙasar na ƙoƙarin haɗa kai da Faransa wurin kawo hargitsi ba shi da tushe ballantana makama.

Ministan yaɗa labarai na Najeriya Mohammed Idris ne ya bayyana haka a wata takadda da ya fitar a yammacin yau a matsayin martani kan wata hira da shugaban mulkin soji na Jamhuriyar Nijar Tchiani ya yi. inda ya zargi Najeriya da ƙoƙarin kawowa ƙasar tsaiko.

Sanarwar ta ce shugaban Najeriya Bola Tinubu a mtsayinsa na shugaban ƙungiyar raya tattalin arzikin kasashen Afrika ta yamma ECOWAS ya nuna shugabanci abin koyi tare da barin ƙofa a buɗe ga Jamhuriyar Nijar duk kuwa da halin da ake ciki na juyin mulki a ƙasar.

Najeriya ta ce a shirye take wurin tabbatar da kyakykyawar alaƙa da zaman lafiya da fahimtar juna da kuma kyautata alaƙar diflomasiyya mai tsohon tarihi dake tsakaninta da Nijar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa dakarun sojin Najeriya haɗin gwiwa da abokanan hulɗarta na samun nasara sosai wurin yaƙi da ta’addanci a yankin, don haka abin mamaki ne ace ƙasar za ta haɗa kai da wata ƙasar waje wurin kawo tsaiko ko rashin zaman lafiya a makwaftan ƙasashe.

Gwamnatin Najeriyar ta ce babu wani jami’inta da ya taɓa goyan bayan ƙungiyoyin ƴan ta’adda ko wata kungiyar ƴan ta’adda wurin kaiwa Nijar hari.

Gwamnatin ƙasar ta ce Najeriya ta tsaye kan kafafunta da cikakken iko kan ƙasar. kuma ba ta taɓa bai wa wata ƙasa dama ko iko na kafa sansanin soji a cikinta ba, sabanin abin da wasu ƙasashe ke yi. Wannan na nuna yadda shugabancin Najeriya ya yi tsayuwar daka wurin tabbatar da  ƴancin ƙasar.

Dangane da zargin da shugaban ƙasar Nijar ya yi cewa ana shirin kawowa bututun mansu da ayyukan gona tazgaro  gwamnatin ta ce kwata-kwata ba gaskiya bane.

Gwamnatin Najeriya ta ce waɗannan zarge-zarge da shugaban mulkin sojin Nijar Abdourahmane Tchiani ya yi tamkar kawar da hankalin jama’a ne kan gazawar da mulkinsa ya yi tun bayan da ya jagoranci juyin mulki. inda gwamnatin ta buƙaci da Jamhuriyar Nijar ta mayar da hankali wurin tattaunawa da haɗa kai maimakon zarge-zarge marasa tushe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp