Home General Bama-baman Lakurawa ne suka kashe mutane a Silame ba harin sojoji ba...

Bama-baman Lakurawa ne suka kashe mutane a Silame ba harin sojoji ba – Sojoji

Rundunar sojin Najeriya ta ce bama-baman da Lakurawa suka ajiye a ƙauyukan da sojojin suka kai wa hari ne suka kashe mutanen gari, ba hare-haren da sojojin suka ƙaddamar ba.

A ranar Labara da safe ne aka samu rahotonnin hare-haren jiragen sojin Najeriya a wasu ƙauyuka biyu da ke yankin ƙaramar hukumar Silame a jihar Sokoto.

Gwamnan jihar, Ahmad Aliyu ya ce sojojin ƙasar ne suka kai harin bisa kuskure, lamarin ya yi sanadin mutuwar mutum 10, wani abu da gwamnan ya danganta da ƙaddara.

To sai dai cikin wata sanarwa da shalkwatar tsaron ƙasar ta fitar mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labaranta, Manjo JanarEdwar Buba ya fitar ya ce ba harin sojojin ne ya kashe mutanen ba.

Ya ce kafin kai harin, sai da sojojin suka ɗauki tsawon lokaci suna gudanar da cikakken bincike ta hanyar tattara bayanan sirri, sanna suka tabbatar da cewa Lakurawa ne ke karakainarsu a yankin.

”Sannan jirginmu ya ƙaddamar da hare-hare kan wuraren da muka tabbatar da cewa na Lakurawa ne da misalin ƙarfe 6:00 na asubahin ranar 25 ga watan Disamba, ta hanyar amfani da ƙananan makamai domin taƙaita ɓarnar da hare-haren za su haifar,” in ji Manjo Janar Edwar Buba.

Ya ƙara da cewa bayan harin dakarunsu da ke ƙasa sun je wurin domin tantance harin.

”Kuma sun tabbatar mana cewa hare-haren sun yi nasara, domin sun lalata maɓoyar Lakurawan, tare da ‘yar ƙaramar ɓarna a ƙauyen. Haka kuma sojojinmu na ƙasa sun zanta da mutanen ƙauyen inda suka tabbatar musu cewa akwai Lakurawa a inda aka kai harin,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa hare-harenmu sun yi nasara wajen kashe Lakurawa a yankin tare da lalata muhimman abubuwan da Lakurawan ke amfani da su ciki har da makamansu.

”Don haka faɗawar harin kan rumbun makaman Lakuwarar ya haifar da wasu ƙarin fashe-fashen bom a wurare daban-daban, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 10, kuma muna kan bincike domin tabbatar da cewa ko suna cikin masu taimaka wa Lakurawan ko akasin haka,” a cewar sojojin na Najeriya.

Sanarwar ta ci gaba da cewa mutanen yankin sun tabbatar musu cewa Lakurawa na gudanar da harkokinsu a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp