Home General Bama-baman Lakurawa ne suka kashe mutane a Silame ba harin sojoji ba...

Bama-baman Lakurawa ne suka kashe mutane a Silame ba harin sojoji ba – Sojoji

Rundunar sojin Najeriya ta ce bama-baman da Lakurawa suka ajiye a ƙauyukan da sojojin suka kai wa hari ne suka kashe mutanen gari, ba hare-haren da sojojin suka ƙaddamar ba.

A ranar Labara da safe ne aka samu rahotonnin hare-haren jiragen sojin Najeriya a wasu ƙauyuka biyu da ke yankin ƙaramar hukumar Silame a jihar Sokoto.

Gwamnan jihar, Ahmad Aliyu ya ce sojojin ƙasar ne suka kai harin bisa kuskure, lamarin ya yi sanadin mutuwar mutum 10, wani abu da gwamnan ya danganta da ƙaddara.

To sai dai cikin wata sanarwa da shalkwatar tsaron ƙasar ta fitar mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labaranta, Manjo JanarEdwar Buba ya fitar ya ce ba harin sojojin ne ya kashe mutanen ba.

Ya ce kafin kai harin, sai da sojojin suka ɗauki tsawon lokaci suna gudanar da cikakken bincike ta hanyar tattara bayanan sirri, sanna suka tabbatar da cewa Lakurawa ne ke karakainarsu a yankin.

”Sannan jirginmu ya ƙaddamar da hare-hare kan wuraren da muka tabbatar da cewa na Lakurawa ne da misalin ƙarfe 6:00 na asubahin ranar 25 ga watan Disamba, ta hanyar amfani da ƙananan makamai domin taƙaita ɓarnar da hare-haren za su haifar,” in ji Manjo Janar Edwar Buba.

Ya ƙara da cewa bayan harin dakarunsu da ke ƙasa sun je wurin domin tantance harin.

”Kuma sun tabbatar mana cewa hare-haren sun yi nasara, domin sun lalata maɓoyar Lakurawan, tare da ‘yar ƙaramar ɓarna a ƙauyen. Haka kuma sojojinmu na ƙasa sun zanta da mutanen ƙauyen inda suka tabbatar musu cewa akwai Lakurawa a inda aka kai harin,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa hare-harenmu sun yi nasara wajen kashe Lakurawa a yankin tare da lalata muhimman abubuwan da Lakurawan ke amfani da su ciki har da makamansu.

”Don haka faɗawar harin kan rumbun makaman Lakuwarar ya haifar da wasu ƙarin fashe-fashen bom a wurare daban-daban, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 10, kuma muna kan bincike domin tabbatar da cewa ko suna cikin masu taimaka wa Lakurawan ko akasin haka,” a cewar sojojin na Najeriya.

Sanarwar ta ci gaba da cewa mutanen yankin sun tabbatar musu cewa Lakurawa na gudanar da harkokinsu a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp