Home General Akwai yiwuwar ƙara kuɗin kira da na data a sabuwar shekarar 2025...

Akwai yiwuwar ƙara kuɗin kira da na data a sabuwar shekarar 2025 a Najeriya

Akwai yuwuwar kamfanonin sadarwa a Najeriya su samu amincewar hukumar da ke kula da su NCC domin su ƙara kuɗin data da na kiran waya a sabuwar shekarar 2025.

Wani babban jami’i da ya nemi a sakaya sunanshi ya ce hukumar sadarwa ta Najeriya NCC ka iya bai wa kamfanonin damar ƙara kuɗi.

Dailytrust ta rawaito cewa dukda tsadar rayuwa ammaanƙi amincewa kamfanonin su ƙara kuɗin kira sama da shekaru 11 da suka gabata.

Kamfanoni kamar MTN da Airtel da 9Mobile sun jima suna miƙa buƙatar ƙarin kuɗin GA Hukumar duba da yanayin tattalin arziki a ƙasar.

Wasu majiyoyin kamfanonin sadarwar sun ce ƙarin da za a fuskanta a ƙasar zai iya kaiwa kaso 40.

Wannan na nufin cewa kiran waya na minti 1 zai tashi daga naira 11 zuwa 15.40, aika sakon kar ta kwana a salula zai tashi daga naira 4 zuwa naira 5.60.

Farashin data 1GB zai tashi daga naira dubu 1 zuwa dubu1 da 400

A ranar 20 ga watan disamba a wata tattaunawa da manema labarai ministan sadarwa na Najeriya Dr. Bosun Tijani ya nuna cewar akwai buƙatar sake duba farashin.

A shekarar 2023 ne kamfanin MTN yayi asarar da ta kai Naira biliyan 137, asarar da ta ƙaru zuwa biliyan 514.9 a watanni 9 na farkon 2024.

Kamfanin Airtel dake aiki a Afrika shima ya sanar da yin asarar da ta kai dala miliyan 89 a 2024 kuma hakan ya biyo ƙaluabalen da yake fuskanta a Najeriya

Kawo lokacin haɗa wannan rahoto babu wani martani daga hukumomin da abin ya shafa a Najeriya

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp