Rundunar sojin Najeriya ta ce bama-baman da Lakurawa suka ajiye a ƙauyukan da sojojin suka kai wa hari ne suka kashe mutanen gari, ba hare-haren da sojojin suka ƙaddamar ba.
Cikin wata sanarwa da shalkwatar tsaron Najeriyar ta fitar mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labaranta, Manjo Janar Edwar Buba ta ce ba harin sojojin ne ya kashe mutanen ba.
Read Also:
Jami’in ya ce kafin kai harin, sai da sojojin suka ɗauki tsawon lokaci suna gudanar da bincike ta hanyar tattara bayanan sirri, kuma sai da suka tabbatar da cewa Lakurawa ne ke kai kawo a yankin kafin afka musu.
A ranar Laraba ne aka samu rahotonnin hare-haren jiragen sojin Najeriya a wasu ƙauyuka biyu da ke yankin ƙaramar hukumar Silame a jihar Sokoto.
Gwamnan jihar, Ahmad Aliyu ya ce sojojin ƙasar ne suka kai harin bisa kuskure, lamarin ya yi sanadin mutuwar mutune 10.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1463 days 25 minutes 56 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 2 hours 7 minutes 21 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com