Home General PDP ta zargi ‘yan APC da satar tiriliyan 25

PDP ta zargi ‘yan APC da satar tiriliyan 25

Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya ta PDP ta nemi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ƙaddamar da bincike kan kuɗaɗe naira tiriliyan 25 da ta zargi ‘yan jam’iyyarsa ta APC da sacewa.

PDP ta yi wannan kira ne a saƙon da ta wallafa na sabuwar shekara, wanda kakakinta na ƙasa Debo Ologuagba ya sanya wa hannu ranar Talata.

“Ya kamata shugaban ƙasa ya wanke kansa game da yaƙi da cin hanci da rashawa ta hanyar ba da umarnin yin bincike da kuma dawo da sama da tiriliyan 25 da aka ce shugabannin APC da jami’an gwamnati sun sace,” in ji sanarwar.

Jam’iyyar ta kuma nemi shugaban ya bayyana adadin kuɗaɗen da gwamnatinsa ta tara daga cire tallafin man fetur da ya yi a watan Mayun 2023.

Haka nan, PDP ta nemi Tinubu ya kawo ƙarshen matsalar tsaro, da yunwa, da kuma ƙarancin man fetur “domin sauƙaƙa wa rayuwar ‘yan Najeriya”.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp