Home General Saƙon Tinubu na sabuwar shekara soki-burutsu ne – PDP

Saƙon Tinubu na sabuwar shekara soki-burutsu ne – PDP

Babbar jam’iyyar hamayya a Najeriya, PDP ta ce jawabin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wa al’ummar kasar na sabuwar shekara, kalaman baka ne kawai.

A jawabin da Tinubun ya yi ranar Laraba 1 ga watan Janairun, 2025, ya bayyana tsare-tsaren da ya ce gwamnatinsa za ta bullo da su domin rage tsadar farashin abinci da samar da tsaro da kuma wasu nasarori da ya ce gwamnatinsa ta samu.

Ya ce duk abubuwan da Tinubun ya fada na cewa gwamnatinsa ta samu nasara, kamata ya yi a ce an gan su a fili muraran, kamar yadda akan ce, ”an ce da kare ana biki a gidanku ya ce to mu gani a kasa.”

Tsauri ya ce duk abubuwan da ya fada ba a takarda ya kamata a gan su ba, yana mai nuni da cewa idan har gaskiya ne gwamnatin ta samu wannan nasara da Tinubun ya fada to jama’a su gani amma lamartin sabanin haka yake.

”Ba abin mamaki ba ne in Shugaban Kasa ya yi wadannan maganganu domin kawai ya sanar da ‘yan Najeriya ba don ya dadada masu ba, don duk abin da ya fadi kowa ya sani ba za a ce karya ba ne amma ba gaskiya ba ne – misali in an ce mana farashin mai ya ragu yaushe ya ragu?” In ji shi.

Ya ce gwamnati na cewa farashin dala ya ragu naira ta kara samun daraja, to amma ya yi nuni da cewa, ” mun wayi gari dala ta koma naira 1600 daga naira 1700, cewa ake an samu nasara, to wace nasara aka samu bayan lokacin da Buhari ya hau mulki muna sayen dala naira tamanin?”

”To wane irin cigaba ne wannan? Mu a wurinmu Turanci ne aka rubuta kuma ya karantu,” in ji shi.

A dangane da kalaman shugaban ne jam’iyyar PDP ta bakin tsohon sakatarenta na kasa Sanata Umaru Tsauri, ta mayar da martani da cewa kalaman soki-burutsu ne kawai.

A tattaunawarsa da BBC, Tsauri ya ce, abubuwan da shugaban ya karanta abin da su suka dauka an rubuta masa Turanci ne kawai ya karanta, amma ba wai abubuwa ne da suke a zahirin gaskiya ba.

Ya ce duk abubuwan da Tinubun ya fada na cewa gwamnatinsa ta samu nasara, kamata ya yi a ce an gan su a fili muraran, kamar yadda akan ce, ”an ce da kare ana biki a gidanku ya ce to mu gani a kasa.”

Tsauri ya ce duk abubuwan da ya fada ba a takarda ya kamata a gan su ba, yana mai nuni da cewa idan har gaskiya ne gwamnatin ta samu wannan nasara da Tinubun ya fada to jama’a su gani amma lamartin sabanin haka yake.

”Ba abin mamaki ba ne in Shugaban Kasa ya yi wadannan maganganu domin kawai ya sanar da ‘yan Najeriya ba don ya dadada masu ba, don duk abin da ya fadi kowa ya sani ba za a ce karya ba ne amma ba gaskiya ba ne – misali in an ce mana farashin mai ya ragu yaushe ya ragu?” In ji shi.

Ya ce gwamnati na cewa farashin dala ya ragu naira ta kara samun daraja, to amma ya yi nuni da cewa, ” mun wayi gari dala ta koma naira 1600 daga naira 1700, cewa ake an samu nasara, to wace nasara aka samu bayan lokacin da Buhari ya hau mulki muna sayen dala naira tamanin?”

”To wane irin cigaba ne wannan? Mu a wurinmu Turanci ne aka rubuta kuma ya karantu,” in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp