Home General Tinubu ya bukaci ‘yan Nijeriya su kara hakuri

Tinubu ya bukaci ‘yan Nijeriya su kara hakuri

Hoton Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce wahalhalu da “sadaukarwar” da ‘yan ƙasar suka yi ba su tashi a banza ba tun bayan hawa mulkinsa a watan Mayun 2023.

Da yake bayani cikin saƙonsa na sabuwar shekara da fadar shugaban ƙasa ta fitar, Tinubu ya ce sabuwar shekarar “za ta kusanta mu da kakkyawar Najeriya da muke ta hanƙoro”.

A cewarsa: “Gare ku ‘yan ƙasa, sadaukarwar da kuka yi cikin wata 19 da suka wuce ba ta tashi a banza ba. Ina tabbatar muku cewa kuma ba za ta tashi a banza ba nan gaba. Mu ci gaba da aikin gina ƙasa tare.”

Tinubu ya kuma jaddada cewa gwamnatinsa za ta ƙara mayar da hankali wajen aiwatarwa da kuma “bijiro da sauye-sauyen da suka zama wajibi” domin haɓaka tattalin arzikin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp