Rikicin kabilanci ya janyo mutuwar mutum tara a Jigawa

Wani rikici da aka danganta da kabilanci wanda ya barke tsakanin kauyukan Gululu da ‘Yan-Kunama a jihar Jigawa, ya yi sanadin mutuwar mutum aƙalla tara.

Rikicin ya samo asali ne sakamakon zargin da aka yi wa wasu matasan Fulani da ɓalle wani shagon kayan masarufi, inda suka yi awon gaba da wasu kayayyaki.

Sai dai zuwa yanzu, an samu nasarar shawo kan rikicin wanda kuma ya janyo asarar gidaje da dama.

Mai magana da yawun ƴan sandan jihar ta Jigawa, DSP Lawan Shi’isu Adam, ya shaida wa BBC cewa tuni aka aika jami’an tsaro karkashin jagorancin kwamishinan ƴan sandan jihar zuwa yankin domin kwantar da hankali.

“Za mu gudanar da bincike don ganin an kama waɗanda suka aikata wannan laifi da kuma hukunta su,” in ji DSP Lawan.

Ya ce hankali ya fara kwanciya a garuruwan kuma jami’an tsaro suna ta kai kawo don tabbatar da cewa ba a sake samun tashin hankali ba.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1486 days 17 hours 30 minutes 41 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1468 days 19 hours 12 minutes 6 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com