Home General Gwamnatin Jihar Kano ta magantu Kan dokar harajin Tinubu

Gwamnatin Jihar Kano ta magantu Kan dokar harajin Tinubu

Gwamnatin Jihar Kano, ta bayyana matsayarta kan sabbin dokokin haraji da ake tattaunawa a Majalisar Dokokin Najeriya.

Mataimakin gwamnan jihar Kano Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, wanda ya wakilci Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya bayyana hakan ne lokacin bikin sabuwar shekarar 2025 da aka gudanar a Filin Mahaha da ke Ƙofar Naisa.

Wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na mataimakin gwamnan Ibrahim Garba Shu’aibu ya fitar, Gwarzo, ya ce “Waɗannan dokokin haraji ba su ne mafita ga matsalolin tattalin arziƙinmu ba”.

Ya ƙara da cewa jihar Kano ba zata yarda da kowace doka da za ta cutar da walwalar al’ummarta ba.

Ya yaba wa jajircewar al’ummar Kano wajen fuskantar ƙalubalen tattalin arziƙi, inda ya ce sam harajin bai dace ba.

Ya ƙara da cewa kamata ya yi gwamnati ta fi mayar da hankali kan yaƙi da talauci da yunwa, musamman a yankin Arewa, wanda ke fama da tsadar rayuwa da rashin tsaro.

Mataimakin Gwamnan, ya na jaddada nasarorin gwamnatin Kano a ɓangarorin lafiya, ilimi, samar da hanyoyi, da tallafin karatu zuwa ƙasashen waje.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp