Home General Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Kwamitin Kula Da Bada Tallafin Jini

Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Kwamitin Kula Da Bada Tallafin Jini

Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano, ta kaddamar da Kwamitin kwararru wadanda zasu kula da ayyukan bada tallafin Jini a fadin jihar.

Kwamishinan lafiya na jihar Kano, Dakta Abubakar Labaran Yusif ne ya jagoranci kaddamar da kwamitin, da nufin samar da tsarin da zai dinga tabbatar da inganci da kuma tsarin da ake bi wajen samar da jini ga marasa lafiyar da suke bukata.

A cewar sa, “Gwamnatin Kano ta dauki matakin ne a kokarin ta na kawo karshen matsalolin da ake fuskanta, wajen tabbatar da kyakkyawan yanayin samar da jini ga marasa lafiya da kuma kulawa da ajiyar sa, adan haka muna yabawa gwamnan Kano a bisa kulawar da yake bawa fannin lafiya a koda yaushe”.

Ya kuma bayyana kyakkyawan zaton da yake dashi na ganin cewar za’a samu nasarar da ake bukata, duba da ƙunshin mambobin kwamitin wanda ya ce an zaɓo su ne bisa cancanta da kwarewar su a fannin kiwon lafiya, harma ya hore su da suyi kokarin sauke nauyin da aka dora musu.

Da yake jawabi, Shugaban kwamitin, kuma Daraktan kula da ayyukan lafiya a hukumar kula da manyan Asibitocin jihar Kano, Dakta Musbahu Rabiu ya godewa Kwamishinan a bisa kyakkyawan zaton da yake musu, harma yasha alwashin cewa kwamitin zai yi aiki tukuru don ganin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Aikin kwamitin shine hada hannu da masu ruwa da tsakin fannin lafiya domin samar da kayan aiki, ledar daukar jinin dama bawa ma’aikata bitar sanin makamar aiki domin inganta fannin.

Mambobin Kwamitin sun kunshi Daraktocin dakunan gwaje-gwaje, Malaman jinya, Daraktan mulki na hukumar kula da manyan Asibitocin jihar Kano, wakilan hukumar kula da Asibitoci masu zaman kansu, dana ma’aikatar lafiya a matakin farko, dama sauran dukkan wasu bangarorin dake da alaka da fannin lafiya a lungu da sako na jihar.

Sanarwar da Jami’in yada labaran Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano Ibrahim Abdullahi ya aiko wa jaridar PRNigeria ta ce, an nada kwararriyar nan a fannin bada tallafin Jini wato Dakta Hauwa Ibrahim a matsayin Sakatariyar kwamitin.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp