Home General Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Kwamitin Kula Da Bada Tallafin Jini

Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Kwamitin Kula Da Bada Tallafin Jini

Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano, ta kaddamar da Kwamitin kwararru wadanda zasu kula da ayyukan bada tallafin Jini a fadin jihar.

Kwamishinan lafiya na jihar Kano, Dakta Abubakar Labaran Yusif ne ya jagoranci kaddamar da kwamitin, da nufin samar da tsarin da zai dinga tabbatar da inganci da kuma tsarin da ake bi wajen samar da jini ga marasa lafiyar da suke bukata.

A cewar sa, “Gwamnatin Kano ta dauki matakin ne a kokarin ta na kawo karshen matsalolin da ake fuskanta, wajen tabbatar da kyakkyawan yanayin samar da jini ga marasa lafiya da kuma kulawa da ajiyar sa, adan haka muna yabawa gwamnan Kano a bisa kulawar da yake bawa fannin lafiya a koda yaushe”.

Ya kuma bayyana kyakkyawan zaton da yake dashi na ganin cewar za’a samu nasarar da ake bukata, duba da ƙunshin mambobin kwamitin wanda ya ce an zaɓo su ne bisa cancanta da kwarewar su a fannin kiwon lafiya, harma ya hore su da suyi kokarin sauke nauyin da aka dora musu.

Da yake jawabi, Shugaban kwamitin, kuma Daraktan kula da ayyukan lafiya a hukumar kula da manyan Asibitocin jihar Kano, Dakta Musbahu Rabiu ya godewa Kwamishinan a bisa kyakkyawan zaton da yake musu, harma yasha alwashin cewa kwamitin zai yi aiki tukuru don ganin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Aikin kwamitin shine hada hannu da masu ruwa da tsakin fannin lafiya domin samar da kayan aiki, ledar daukar jinin dama bawa ma’aikata bitar sanin makamar aiki domin inganta fannin.

Mambobin Kwamitin sun kunshi Daraktocin dakunan gwaje-gwaje, Malaman jinya, Daraktan mulki na hukumar kula da manyan Asibitocin jihar Kano, wakilan hukumar kula da Asibitoci masu zaman kansu, dana ma’aikatar lafiya a matakin farko, dama sauran dukkan wasu bangarorin dake da alaka da fannin lafiya a lungu da sako na jihar.

Sanarwar da Jami’in yada labaran Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano Ibrahim Abdullahi ya aiko wa jaridar PRNigeria ta ce, an nada kwararriyar nan a fannin bada tallafin Jini wato Dakta Hauwa Ibrahim a matsayin Sakatariyar kwamitin.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp