Home General Rikicin kabilanci ya janyo mutuwar mutum tara a Jigawa

Rikicin kabilanci ya janyo mutuwar mutum tara a Jigawa

Wani rikici da aka danganta da kabilanci wanda ya barke tsakanin kauyukan Gululu da ‘Yan-Kunama a jihar Jigawa, ya yi sanadin mutuwar mutum aƙalla tara.

Rikicin ya samo asali ne sakamakon zargin da aka yi wa wasu matasan Fulani da ɓalle wani shagon kayan masarufi, inda suka yi awon gaba da wasu kayayyaki.

Sai dai zuwa yanzu, an samu nasarar shawo kan rikicin wanda kuma ya janyo asarar gidaje da dama.

Mai magana da yawun ƴan sandan jihar ta Jigawa, DSP Lawan Shi’isu Adam, ya shaida wa BBC cewa tuni aka aika jami’an tsaro karkashin jagorancin kwamishinan ƴan sandan jihar zuwa yankin domin kwantar da hankali.

“Za mu gudanar da bincike don ganin an kama waɗanda suka aikata wannan laifi da kuma hukunta su,” in ji DSP Lawan.

Ya ce hankali ya fara kwanciya a garuruwan kuma jami’an tsaro suna ta kai kawo don tabbatar da cewa ba a sake samun tashin hankali ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp