Bankin China ya bai wa Najeriya rancen kuɗin gina titin jirgi na Kano zuwa Kaduna

Bankin raya ƙasa na China ya bai wa Najeriya rancen dala miliyan 254.76 domin gina titin jirgin ƙasa daga Kano zuwa Kaduna.

Sanarwar da bankin ya fitar na zuwa ne gabanin ziyarar ministan harkokin wajen China a Najeriya cikin mako mai zuwa.

Minista Wang Yi zai isa Najeriya domin ganawa da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, da sauran manyan jami’an gwamnatin tarayya tun daga ranar Laraba.

Aikin layin dogon mai tsawon kilomita 203, ana sa ran zai laƙume dala miliyan 973 amma ya dakata saboda ƙarancin kuɗi.

“Idan aka kammala shi, layin dogon zai haɗe Kano, mai muhimmanci a arewacin Najeriya, da kuma Abuja babban birnin ƙasar, inda zai ba wa mutane damar yin tafiya mai sauƙi,” a cewar sanarwar da bankin ya wallafa a shafinsa na intanet.

Tun da farko gwamnatin Najeriya ta ce Exim Bank na China zai ɗauki nauyin aikin a 2020, amma sai ya janye.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 19 hours 35 minutes 31 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 21 hours 16 minutes 56 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com