Home General Gwamnan Kano ya mayar wa ‘yan APC martani kan zaɓen 2027

Gwamnan Kano ya mayar wa ‘yan APC martani kan zaɓen 2027

Gwamnan jihar Kano da ke arewacin Najeriya, Abba Kabir Yusuf, ya ce aikin hidimta wa Kano ne a gabansa yanzu “ba neman wa’adin mulki na biyu ba”.

Gwamnan na mayar da martani ne game da kalaman da tsohon shugaban jam’iyyar APC na Kano, Abdullahi Abbas, ya yi a farkon makon nan game da shirinsu na ƙwace mulkin jihar daga jam’iyyar NNPP a zaɓen 2027.

Kakakin gwamnatin jihar ta Kano, Sanusi Dawakin Tofa, ya faɗa cikin wata sanarwa cewa gwamnan ya yi martanin ne yayin taron tallafa wa mata a fadar gwamnatin jihar.

“Ba neman wa’adi na biyu ne ya fi damu na ba. Na fi damuwa da sauke nauyin alƙawurran da na ɗauka a wa’adin farko…kuma ina son mutanen Kano su yi min hukunci da ayyukana a ƙarshen mulkin,” a cewar gwamnan.

Jam’iyyar NNPP ta ƙwace mulkin Kano ne a zaɓen 2023 bayan APC ta yi wa’adin mulki biyu na shekara takwas ƙarƙashin Abdullahi Umar Ganduje.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp