China ta yi alƙawarin taimaka wa Najeriya a fannin tsaro da tattalin arziki

Najeriya da China sun amince su ƙarfafa haɗin gwiwa a fannin makamashi, da tsaro, da harkokin kuɗi, kamar yadda ministocin harkokin wajen ƙasashen sukam bayyana yau Alhamis.

Ministan Harkokin Wajen China Wang Yi na ziyara a Najeriya ne a matsayin wani ɓangare na ziyarar aiki a ƙasashen Afirka huɗu domin faɗaɗa tasirin ƙasarsa a nahiyar.

Mista Wang ya ce China za ta duba buƙatar da Najeriya ta gabatar mata ta faɗaɗa yarjejniyar amfani da takardun kuɗin ƙasar na Yan.

A ɓangaren tsaro kuma, Wang ya ce China za ta dinga goya wa Afirka baya kodayaushe a zauren tsaron tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya.

“Za mu yi aiki da Afirka wajen inganta tsaro da kuma cim ma zaman lafiya ta hanyar ayyukan more rayuwa,” in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com