Najeriya da China sun amince su ƙarfafa haɗin gwiwa a fannin makamashi, da tsaro, da harkokin kuɗi, kamar yadda ministocin harkokin wajen ƙasashen sukam bayyana yau Alhamis.
Ministan Harkokin Wajen China Wang Yi na ziyara a Najeriya ne a matsayin wani ɓangare na ziyarar aiki a ƙasashen Afirka huɗu domin faɗaɗa tasirin ƙasarsa a nahiyar.
Mista Wang ya ce China za ta duba buƙatar da Najeriya ta gabatar mata ta faɗaɗa yarjejniyar amfani da takardun kuɗin ƙasar na Yan.
A ɓangaren tsaro kuma, Wang ya ce China za ta dinga goya wa Afirka baya kodayaushe a zauren tsaron tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya.
“Za mu yi aiki da Afirka wajen inganta tsaro da kuma cim ma zaman lafiya ta hanyar ayyukan more rayuwa,” in ji shi.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1488 days 8 hours 54 minutes 56 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1470 days 10 hours 36 minutes 21 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com