Home General Gwamnatin Najeriya ta buɗe kwalejin horas da matasa kan ƙirƙirarriyar basira a...

Gwamnatin Najeriya ta buɗe kwalejin horas da matasa kan ƙirƙirarriyar basira a kyauta

Gwamnatin Najeriya ta ce ta ƙaddamar da wani shiri na horar da matasa game da sanin makamar ƙirƙirarriyar basira wato Artificial Intelligence (AI) ta intanet.

Ministan Ƙirƙira, Kimiyya da Fasaha Uche Geoffrey Nnaji ya ce shirin wanda aka ƙaddamar ranar Talata, an yi masa suna AI Academy – wato kwalejin ƙirƙirarriyar basira.

Najeriya ta ƙaddamar da shirin bisa haɗin gwiwa da ƙungiyar ƙasashe rainon Ingila ta Commonwealth.

“AI Academy za ta horar da ɗalibai, da matasa, da ma’aikatan gwamnati wajen shawo kan matsaloli da kuma ƙirƙirar damarmaki ta hanyar amfani da ƙirƙirarriyar basira,” in ji ministan.

Ya ƙara da cewa za a rufe yin rajista a shafin kwalejin ranar 30 ga watan Janairun nan.

Ministan ya ce masu sha’awa na iya a ziyartar wannan adireshin an domin yin rajista.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a Jihar
X whatsapp