Home General Gwamnatin Tinubu ba ta aiwatar da kasafin kudin bara ba da kyau...

Gwamnatin Tinubu ba ta aiwatar da kasafin kudin bara ba da kyau – Majalisar Dokoki

Majalisar dokokin Najeriya ta bayyana damuwa game da babban rashin daidaito tsakanin kudaden da akan kashe wajen ayyukan raya kasa da wadanda akan kashe don gudanar da ayyukan ma’aikatu na yau da kullum a kasafin kudin bara.

‘Yan majalisar sun yi nuni da yadda aka yi kwauron sakin kudi don aiwatar da manyan ayyukan raya kasa ga ma’aikatu da sassa da hukumomin gwamnati.

‘Yan majalisar dokokin sun ce abin da aka samu bai taka kara ya karya ba, kuma ba zai kai a ce an gudanar da ayyukan yadda ya dace ba a kasafin kudin na bara.

Daya daga cikin ‘yan majalisar Injiniya Satomi Ahmed, ya shaida wa BBC cewa an yi shirin aiwatar da karashen kasafin kudin na bara har zuwa watan Yunin bana, ta yadda za a rika aiwatar da shi tare da na wannan shekara.

Yace : “Babbar damuwar ita ce rashin fitar da kudaden da ya kamata a yi manyan ayyuka na ci gaban kasa, rashin hakan shi ne ya haifar da halin da Najeriya ke ciki, da rashin ci gaban gwamnati da matsalolin da ta ke fuskanta.

Ba a bai wa ma’aikatu daban-daban kudaden aiwatar da ayyuka na musamman, kamar fannin noma da ta ttalin arziki, da ma’aikatar raya yankin Arewa maso yammacin Najeriya ba.

Wasu ma’aikatun sun samu kashi 40, wasu kuma kashi 30 cikin 100, kai akwai wasu ma da ba su samu kashi 20 ba a kasafin kudin shekarar 2024,” in ji Satomi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp