Home General Gwamnatin Tinubu ba ta aiwatar da kasafin kudin bara ba da kyau...

Gwamnatin Tinubu ba ta aiwatar da kasafin kudin bara ba da kyau – Majalisar Dokoki

Majalisar dokokin Najeriya ta bayyana damuwa game da babban rashin daidaito tsakanin kudaden da akan kashe wajen ayyukan raya kasa da wadanda akan kashe don gudanar da ayyukan ma’aikatu na yau da kullum a kasafin kudin bara.

‘Yan majalisar sun yi nuni da yadda aka yi kwauron sakin kudi don aiwatar da manyan ayyukan raya kasa ga ma’aikatu da sassa da hukumomin gwamnati.

‘Yan majalisar dokokin sun ce abin da aka samu bai taka kara ya karya ba, kuma ba zai kai a ce an gudanar da ayyukan yadda ya dace ba a kasafin kudin na bara.

Daya daga cikin ‘yan majalisar Injiniya Satomi Ahmed, ya shaida wa BBC cewa an yi shirin aiwatar da karashen kasafin kudin na bara har zuwa watan Yunin bana, ta yadda za a rika aiwatar da shi tare da na wannan shekara.

Yace : “Babbar damuwar ita ce rashin fitar da kudaden da ya kamata a yi manyan ayyuka na ci gaban kasa, rashin hakan shi ne ya haifar da halin da Najeriya ke ciki, da rashin ci gaban gwamnati da matsalolin da ta ke fuskanta.

Ba a bai wa ma’aikatu daban-daban kudaden aiwatar da ayyuka na musamman, kamar fannin noma da ta ttalin arziki, da ma’aikatar raya yankin Arewa maso yammacin Najeriya ba.

Wasu ma’aikatun sun samu kashi 40, wasu kuma kashi 30 cikin 100, kai akwai wasu ma da ba su samu kashi 20 ba a kasafin kudin shekarar 2024,” in ji Satomi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 
X whatsapp