Home General Gwamnatin Najeriya ta buɗe kwalejin horas da matasa kan ƙirƙirarriyar basira a...

Gwamnatin Najeriya ta buɗe kwalejin horas da matasa kan ƙirƙirarriyar basira a kyauta

Gwamnatin Najeriya ta ce ta ƙaddamar da wani shiri na horar da matasa game da sanin makamar ƙirƙirarriyar basira wato Artificial Intelligence (AI) ta intanet.

Ministan Ƙirƙira, Kimiyya da Fasaha Uche Geoffrey Nnaji ya ce shirin wanda aka ƙaddamar ranar Talata, an yi masa suna AI Academy – wato kwalejin ƙirƙirarriyar basira.

Najeriya ta ƙaddamar da shirin bisa haɗin gwiwa da ƙungiyar ƙasashe rainon Ingila ta Commonwealth.

“AI Academy za ta horar da ɗalibai, da matasa, da ma’aikatan gwamnati wajen shawo kan matsaloli da kuma ƙirƙirar damarmaki ta hanyar amfani da ƙirƙirarriyar basira,” in ji ministan.

Ya ƙara da cewa za a rufe yin rajista a shafin kwalejin ranar 30 ga watan Janairun nan.

Ministan ya ce masu sha’awa na iya a ziyartar wannan adireshin an domin yin rajista.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp