Kotun daukaka kara a Abuja ta yanke hukunci kan dambarwar Masarautar Kano

Kotun daukaka kara dake zaman ta a Abuja ta yanke hukuncin cewa babbar kotun tarayya ba ta da hurumin saurarar duk wata kara da ta shafi dokar masarautu.

Haka zalika kotun ta ce sashi na 251 na kundin tsarin mulkin Nijeriya ya yayi bayani dalla-dalla kan harancin kotun tarayya ta shiga al’amarin da ya shafi masarautu.

Kotun tace tsohon sarkin na kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya gaza gabatar da hujjojin da za su gasgata da’awarsa na cewa an tauye masa hakkinsa matsayin sa na dan Adam.

Idan za a iya tunawa Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero bayan da gwamnatin Kano ta ayyana cire shi, ya garzaya gaban babbar kotun tarayya dake Kano domin kalubalantar matakin gwamnatin.

Aminu Ado Bayero yana da’awar cewa an take masa hakkinsa a matsayinsa na dan adam, don haka yake neman kotun da duba labarin, sai dai gwamnatin Kano ta ce kotun tarayyar bata da hurumin saurarar kara lamarin da yasa ta tafi kotun daukaka kara domin nemo fassara.

Kotun daukaka Karar ta ce Babbar kotun tarayyar ba ta da hurumin kamar yadda kotun koli ta Kasa ta taba yanke hukuncin akan shari’ar Tukur da gwamnan gongola.

Kotun ta ce kotun da ke da hurumin shari’ar masarautu a tsarin mulkin Nijeriya, ita ce babbar kotun jiha ba babbar kotun tarayya ba.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1464 days 4 hours 54 minutes 48 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1446 days 6 hours 36 minutes 13 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com