Gwamnatin jihar Kano, ta nuna Jin dadinta da hukuncin da kotun daukaka kara da ke Abuja ta yanke dangane da batun da ya shafi Masarautar Kano na dawo Mai Martaba Khalifa Muhammadu Sanusi na biyu.
Kwamishinan shari’a na Jihar Kano Barrister Haruna Isah Dediri ya bayyana gamsuwarsa Lokacin da ya ke ganawa da manema labaru.
Dederi ya ce Hukuncin da kotun daukaka karar ta yi, ya soke hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke a baya, ya kuma tabbatar da matakin da gwamnatin Kano ta dauka dangane da nade-nade, mukamai da Kuma gyare-gyare a masarautar Kano.
Read Also:
”Duk wasu hukunce-hukunce da babbar kotun tarayya ta yi a baya wadanda suka shafi rikicin masarautu a Kano ya zama rusashshe, idan kai la’akari da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke a jiya”. Inji Barr. Dederi
Dederi ya ce a madadin gwamnatin jihar Kano suna yabawa bangaren shari’a na kasar nan saboda yadda ya yanke hukuncin ba tare da daukar wani bangare ba, dangane da rikicin masarautu a Kano.
“Da wannan hukuncin za gwamnatin jihar Kano za ta tabbatar da cigaba da aiki kafa da kada da masarautun gargajiya domin ciyar da jihar Kano gaba ta kowacce fuska”. A cewar Kwamishinan shari’a
Daderi ya yi kira da hukumomi da ma’aikatun gwamnati da kamfanoni da Kungiyoyi da daidaikun al’umma da su tabbatar da bin umarnin da kotun daukaka kara ta yi na tabbatar da abun da gwamnatin Kano ta yi akan abun da ya shafi Masarautar Kano.
Ya ce gwamnatin Kano tana kira ga dukkanin bangarorin da abun ya shafa da su Ajiye komai su zo a hada hannu da su don cigaban jihar Kano.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1464 days 4 hours 43 minutes 45 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1446 days 6 hours 25 minutes 10 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com