Home General Sojoji sun ce sun lalata sansanin Bello Turji tare da kashe ‘yanbindiga...

Sojoji sun ce sun lalata sansanin Bello Turji tare da kashe ‘yanbindiga 25

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta samu nasarar lalata sansanin gawurtaccen ɗan bindigar nan Bello Turji a yankin Fakai na ƙaramar hukumar Shinkafi.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar da ke yaƙi da ‘yanbindiga a arewa maso yamma ‘Operation Fansan Yamma’ ya fitar, ya ce dakarun sojin sun ƙaddamar da hare-haren ne kan maɓoyar ‘yanbindigar a ranar 10 ga watan Janairu.

”Bisa taimakon dakarun sojin sama, mun samu nasarar lalata sansanonin wasu ‘yanbindiga a yankin Fakai na ƙaramar hukumar Shinkafi”, in ji sanarwar.

Ya ƙara da cewa daga cikin sansanonin da aka lalata har da na Bello Turji da Mallam Ila, inda aka kashe ‘yanbindiga 25 tare da raunata fiye da 18.

Haka ma ya ce a lokacin samamen sojojin sun kuɓutar da mutum bakwai da ‘yanbindigar suka yi garkuwa da su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp