Home General Wutar lantarkin Najeriya ta ɗauke gaba ɗaya karon farko a sabuwar shekara

Wutar lantarkin Najeriya ta ɗauke gaba ɗaya karon farko a sabuwar shekara

Najeriya ta sake tsunduma cikin duhu bayan faɗuwar babban layin samar da wutar lantarki na ƙasa, da yammacin ranar Asabar.

Wannan ɗaukewa ita ce karo na farko a shekarar 2025, amma karo na 13 cikin watanni 13 da suka gabata.

Rahotanni sun nuna cewa wutar lantarki ta fara raguwa daga megawat 2,111.01 da misalin ƙarfe 2 na rana.

Daga bisani ta sauka zuwa megawat 390.20 da misalin ƙarfe 3 na rana.

A shekarar da ta gabata, layin samar da wutar lantarkin ya lalace sau 12, wanda hakan ya jefa miliyoyin ’yan Najeriya cikin duhu tare da kawo cikas ga tattalin arziƙi da rayuwar yau da kullum.

Wannan lalacewar na zuwa ne kwanaki 11 kacal da shiga sabuwar shekarar 2025.

Hakan ya sake nuna yadda matsalar rashin ingantaccen tsarin samar da wutar lantarki ke ta’azzara a ƙasar.

Al’ummar Najeriya dai na ci gaba da fuskantar ƙalubale a fannin samar da wutar lantarki, wanda ke da matuƙar tasiri a harkokin kasuwanci, masana’antu, da rayuwar yau da kullum.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp