Home General Rikicin shugabanci ya janyo zanga-zanga a ofishin jam’iyyar PDP

Rikicin shugabanci ya janyo zanga-zanga a ofishin jam’iyyar PDP

Gomman masu zanga-zanga sun yi dafifi a shelkwatar jam’iyyar PDP ta ƙasa da ke Abuja domin nuna rashin amincewa da kama aikin sabon sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sunday Ude-Okoye wanda kotun ɗaukaka ƙara ta ayyana a matsayin sakataren jam’iyyar, kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Bayanai sun nuna cewa shelkwatar jam’iyyar ta tafi hutun ƙarshen shekara ne a watan Disamba inda kuma a ranar Litinin ake sa ran komawa aiki ranar da sabon sakataren zai kama aiki.

To sai dai masu zanga-zanga da ke goyon bayan senator Sam Anyanwu wanda ake taƙaddama a kansa sun mamaye ƙofar ofishin inda suke ta ihun cewa ” ofishin sakataren jam’iyyar PDP na ƙasa akwai mai shi kuma senator Anyanwu ne sakataren.”

A baya-bayan nan ne dai kotun ɗaukaka ƙara ta Enugu ce ta ayyana cewa Sunday Ude-Okoye ne sakataren jam’iyyar halastacce.

An jibge jami’an tsaro a ƙofar shelkwatar jam’iyyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp