Ana Fargabar Mutane Da Yawa Sun Mutu A Gobarar Tankar Mai A Naija

Ana fargabar mutane da dama sun rasu wasu kuma sun jikkata, a yayin da suke kokarin dibar man fetur daga wata tankar mai da ta fadi a kwanar Dikko da ke babban titin Abuja zuwa Kaduna, a jihar Naija.

Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne a yau Asabar, a lokacin da tankar da ke gudu ta fadi man ya zube, mutane suka je suna kwasar man sai motar ta yi bindiga wuta ta tashi.

Wutar ta kone mutane da dama da ke kwasar man yayin da wadanda suke nesa da ita kuwa suka ji rauni.

Kakakin gwamnan jihar Naija, Bologi Ibrahim, ya tabbatar wa da Emergency Digest faruwar lamarin, harma ya ce Gwamnan jihar Mohammed Bago, ya nuna alhininsa a kan Iftila’in.

A karshe ya umarci jami’an tsaro su tabbatar da tsaro a wajen, sannan sauran hukumomin gwamnatin jihar su yi abin da ya wajaba a kai.

Ko a watan Oktobar shekarar da ta wuce an sami makamancin wannan Iftila’i a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura ta jihar Jigawa, inda sama da mutum 170 suka mutu, baya ga jikkatar sama da 50, a sakamakon fashewar tankar, lokacin da wasun su ke kwasar mai.

 

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1464 days 1 hour 16 minutes 27 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1446 days 2 hours 57 minutes 52 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com