Home General Ana Fargabar Mutane Da Yawa Sun Mutu A Gobarar Tankar Mai A...

Ana Fargabar Mutane Da Yawa Sun Mutu A Gobarar Tankar Mai A Naija

Ana fargabar mutane da dama sun rasu wasu kuma sun jikkata, a yayin da suke kokarin dibar man fetur daga wata tankar mai da ta fadi a kwanar Dikko da ke babban titin Abuja zuwa Kaduna, a jihar Naija.

Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne a yau Asabar, a lokacin da tankar da ke gudu ta fadi man ya zube, mutane suka je suna kwasar man sai motar ta yi bindiga wuta ta tashi.

Wutar ta kone mutane da dama da ke kwasar man yayin da wadanda suke nesa da ita kuwa suka ji rauni.

Kakakin gwamnan jihar Naija, Bologi Ibrahim, ya tabbatar wa da Emergency Digest faruwar lamarin, harma ya ce Gwamnan jihar Mohammed Bago, ya nuna alhininsa a kan Iftila’in.

A karshe ya umarci jami’an tsaro su tabbatar da tsaro a wajen, sannan sauran hukumomin gwamnatin jihar su yi abin da ya wajaba a kai.

Ko a watan Oktobar shekarar da ta wuce an sami makamancin wannan Iftila’i a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura ta jihar Jigawa, inda sama da mutum 170 suka mutu, baya ga jikkatar sama da 50, a sakamakon fashewar tankar, lokacin da wasun su ke kwasar mai.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp