Dakarun Najeriya da suke aikin soji na musamman Fansan Yamma sun ce sun kashe ƴandinga da dama, ciki har da ɗan cikin Turji a wani samame da suka kai a sansanin ɗanbindigar.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin hedkwatar taron Najeriya, Edward Buba ya fitar, inda ya ce, “a ranar 17 ga Janairu, dakarun Fansan Yamma sun kutsa dazukan da ke yankin Shinkafi da Kagara da Fakai da Moriki da Maiwa da Chindo, inda suka kashe gomman ƴanbindiga, sannan suka kashe ɗan cikin Bello Turji a Fakai, inda yake ɓoyewa.”
Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin sun samu ƙashe ƴanbindiga da dama, da ɓarnata ma’ajiyarsu, “sannan sun ceto wasu waɗanda Bello Turji ya yi garkuwa da su, bayan ya tsere.”
Sanarta ta ce sojojin sun kai wani samamen a sansanin wani ɗanbindigar mai suna Idi Mallam, “inda sojoji suka kashe ƴanbindiga 3, da kama mutum 3 da ake zargi da taimakon ƴanbindiga, tare da ƙwato wasu makamai da dabbobin da suka sace.”
A ƙarshe Buba ya ce sojojin za su cigaba da fatattarkar ƴanbindigar a ƙoƙarinsu na tabbatar da zaman lafiya a faɗin ƙasar.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1464 days 1 hour 17 minutes 29 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1446 days 2 hours 58 minutes 54 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com