Home General Alamu na nuna yiwuwar Najeriya za ta ga ƙarancin mahajjata a bana

Alamu na nuna yiwuwar Najeriya za ta ga ƙarancin mahajjata a bana

Alƙaluma na nuna yiwuwar Najeriya ta fuskanci ƙarancin maniyyata a hajjin bana, wanda ke da nasaba da hauhawar farashin kujerar hajjin bisa bayanan da hukumar kula da aikin hajji ta ƙasar NAHCON ta fitar a rana Litinin.

Hankula sun tashi matuƙa bayan da hukumar aikin hajjin Najeriyar ta fitar da farashin kujerar ta bana wanda ya tasamma miliyan 8 da rabi a wasu yankunan har ya zarta hakan.

Dai dai lokacin da ya rage ƙasa da wata guda kan wa’adin da NAHCON ta bayar wajen kammala biyan kudin aikin hajjin na bana, har yanzu ana ganin ƙarancin mutanen da ke miƙa kuɗinsu don sayen kujerun aikin hajjin na bana wanda alƙaluman ke nuna yiwuwar ya iya zama hajji mafi ƙarancin jama’a daga Najeriyar.

Alƙaluman farashin da NAHCON ta fitar ya nuna cewa mahajjata daga kudancin ƙasar za su biya tsabar kudi har naira miliyan 8 da dubu 700 yayinda maniyyata da arewa maso gabashin Najeriya kuma za su biya naira miliyan 8 da dubu 300 a gefe guda mahajjata daga arewaci kuma za su biya naira miliyan 8 da dubu 400.

Shugaban hukumar ta NAHCON farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayyana cewa hukumar ta yi aiki tuƙuru wajen ganin farashin hajjin a bana bai kai naira miliyan 9 ba.

A baya dai an yi fargabar farashin aikin hajjin a bana ya iya kai naira miliyan 10 musamman lura da karyewar darajar takardar kudi ta Najeriyar naira.

Ƙarƙashin dokokin hukumar NAHCON dai dukkanin maniyyacin da ya gaza biyan adadin kudin aikin hajjin kafin nan da ranar 5 ga watan Fabarairu kai tsaye sai dai ya jira zuwa shekara mai zuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp