Najeriya ta buƙaci a samar da ƙasashen Isra’ila da Falasɗinu masu cin gashin kansu

Najeriya ta yi kira da a samar da ƙasashen Isra’ila da Falasɗinu masu cin gashin kansu, inda ta ce hakan ne zai wanzar da zaman lafiya a yankin.

Ƙasar ta bayyana haka ne a lokacin da take maraba da tsagaita wuta da aka yi a Gaza tsakanin Isra’ila da Hamas.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, Kimiebi Ebienfa ne ya bayyana haka a zantawarsa da tashar Channels mai zaman kanta a Najeriya.

“Najeriya na kira ga dukkan ɓangarori su haɗa kai domin tabbatar da an cimma sauran matakan yarjejeniyar tsagaita wutar, sannan Najeriya na kira da a samar da ƙasashen biyu na Isra’ila da Falasɗinu masu cin gashin kansu a matsayin hanya ɗaya tilo da za a tabbatar da zaman lafiya a yankin,” in ji Ebienfa.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1464 days 45 minutes 42 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1446 days 2 hours 27 minutes 7 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com