Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya ta yi kira ga ƴan Najeriya su fara shirye-shiryen dakatar da amfani da kamfanoninin sadarwa domin nuna adawarsu ga amincewa da ƙarin kashi 50 na kuɗin kira da data da gwamnatin tarayya ta yi.
A wata sanarwa da NLC ta fitar a jiya Laraba, ta ce ƙarin kuɗin rashin adalci ne ga ƴan ƙasar, waɗanda a yanzu haka suke fuskantar ƙalubale saboda matsin tattalin arziki.
Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya bayyana damuwarsa kan ƙarin, inda ya ce, “wannan matakin, wanda ya zo a daidai lokacin da ma’aikata da sauran ƴan ƙasa suke fama da matsin tattalin arziki, tamkar ba kamfanonin sadarwar wuƙa da nama su yi yadda suke su da ƴan ƙasar, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
“Harkokin sadarwa na cikin abubuwa masu muhimmanci domin sadarwa da neman labarai. Kuma ko a yanzu ma ƙaramin ma’aikacin Najeriya yakan kashe kusan kashi 10 na albashinsa wajen sayan katin waya da data. Misali ma’aikacin da ke karɓar albashin naira 70,000, idan yana kashe naira 7,000 ne, yanzu zai fara kashe kusan naira 10,500 ne a waya.”
Ya kuma caccaki gwamnatin bisa yadda ta amince da ƙarin cikin gaggawa, amma ta ɗauki dogon lokaci kafin ta amince da mafi ƙarancin albashi.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1463 days 18 hours 50 minutes 2 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 20 hours 31 minutes 27 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com