Home General Najeriya ta buƙaci zama mamba a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya

Najeriya ta buƙaci zama mamba a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya

Najeriya ta bukatar kasancewar ta mamba a hukumar sulhu ta Majalisar Ɗinkin Duniya a yayi taron duba lamuran tattalin arziki na duniya wato DAVOS 2025 wanda ke gudana a Switzeland.

Ministan harkokin Najeriya Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ne ya nuna buƙatar ganin Najeriya ta kasance cikikkaiyar mamba ta hukumar sulhi ta Majalisa Ɗinkin Duniya, a yayin da yake bayyana tasirin ƙasar ke dashi wajen wakiltar nahiyar Afika a hukumar.

Da yake jawabi a yayin wani taron tattaunawa mai taken “tasirin Afika” a taron duba tattalin arzikin duniya da aka yi a birnin Davos na kasar Sweden a ranar 21 ga watan Janairun 2025, ministan ya koka ga  kwamitin sulhu ta MDD bisa rashin Afirka a cikin hukumar, yayin da yake bayyana cewa kusan kashi 60 cikin 100 na kudurorin majalisar sun shafi batutuwa masu alaka da Afirka.

Ya kuma yi nuni da cewa, da yawa daga cikin dokokin da Majalisar ta fitar na da illa ga nahiyar ta Afirka, ciki har da dokar sare dazuzzuka, wadda ta haramta sayen amfanin gona daga yankunan da aka sare dazuka, tare da yin watsi da kamfanonin fasaha da ke kera na’urorin da ke ba da damar sare dazuka a nahiyar.

Tuggar ya ƙara da cewa, ƙarƙashin mulkin shugaban Najeriya Bola Tinubu Kasar ta samu ingantuwar lamura kuma duniya ta shaida.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp