Home General Ƙara kuɗin kira da na data rashin adalci ne- NLC

Ƙara kuɗin kira da na data rashin adalci ne- NLC

Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya ta yi kira ga ƴan Najeriya su fara shirye-shiryen dakatar da amfani da kamfanoninin sadarwa domin nuna adawarsu ga amincewa da ƙarin kashi 50 na kuɗin kira da data da gwamnatin tarayya ta yi.

A wata sanarwa da NLC ta fitar a jiya Laraba, ta ce ƙarin kuɗin rashin adalci ne ga ƴan ƙasar, waɗanda a yanzu haka suke fuskantar ƙalubale saboda matsin tattalin arziki.

Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya bayyana damuwarsa kan ƙarin, inda ya ce, “wannan matakin, wanda ya zo a daidai lokacin da ma’aikata da sauran ƴan ƙasa suke fama da matsin tattalin arziki, tamkar ba kamfanonin sadarwar wuƙa da nama su yi yadda suke su da ƴan ƙasar, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

“Harkokin sadarwa na cikin abubuwa masu muhimmanci domin sadarwa da neman labarai. Kuma ko a yanzu ma ƙaramin ma’aikacin Najeriya yakan kashe kusan kashi 10 na albashinsa wajen sayan katin waya da data. Misali ma’aikacin da ke karɓar albashin naira 70,000, idan yana kashe naira 7,000 ne, yanzu zai fara kashe kusan naira 10,500 ne a waya.”

Ya kuma caccaki gwamnatin bisa yadda ta amince da ƙarin cikin gaggawa, amma ta ɗauki dogon lokaci kafin ta amince da mafi ƙarancin albashi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp