Home General Dubu 55 muka sayi ko wacce akuya ba dubu 350 – Gwamnan...

Dubu 55 muka sayi ko wacce akuya ba dubu 350 – Gwamnan Kano

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ake yadawa cewa ta sayi kowacce akuya cikin awakin da zata rabawa matan karkarkara a wani bangare na yunkurin gwamnatin jihar na tallafa musu kan farashin naira dubu 350.

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Waiya, ne ya bayyana hakan ta cikin wani sakon murya da ya aike da manema labarai a yau Alhamis a birnin Kano.

Waiya ya ce an siyi Akuyoyi guda dubu 7158 kan kudi naira miliyan 451, inda za a raba wa mutane dubu 2386, sai Raguna guda 1975 kan kudi naira miliyan 351 da dudu 750 da za raba su ga mutane 987.

Haka zalika an siyi Shanu guda 1400 kan kudi naira biliyan 1 da miliyan 120 wadanda za a raba wa mutane 700, sai kuma kudin ciyarwa da magani da sauran hidinhimu da aka ware na naira miliyan 427 da dubu 958.

Kwamishinan ya kara da cewa jimullar kudin da aka ware sune naira Biliyan 2 da naira miliyan 350 sabanin abinda ake yada wa kan cewar kowacce akuya an siye ta kan naira dubu 350.

‘’’wannan shi ne abunda aka ware ko aka yi da su wato naira miliyan dubu 2 da naira miliyan 350 sabanin abinda mutane suke ta yamadidi da shi’’ Waiya.

Sai dai waiya ya yi zargin cewa an yada labarin da gangan dan a bata gwamnati har ya shawarci manema labarai su dinga bincike kafin su yada wani abu don kaucewa yada fitina a tsakanin al’umma.

‘’Wannan ba daidai ba ne yakamata al’umma su dinga jin tsoron Allah kan abubuwan da suke yi kuma su fahimci cewa ya madidi da abinda yake na zance na karya ba daidai ba ne’’ Waiya’’.

A karshe Waiya ya ce duk wanda ya duba jawabin gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana dukkan adadin kudaden da aka yi daki-daki.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp