Najeriya ta bukatar kasancewar ta mamba a hukumar sulhu ta Majalisar Ɗinkin Duniya a yayi taron duba lamuran tattalin arziki na duniya wato DAVOS 2025 wanda ke gudana a Switzeland.
Ministan harkokin Najeriya Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ne ya nuna buƙatar ganin Najeriya ta kasance cikikkaiyar mamba ta hukumar sulhi ta Majalisa Ɗinkin Duniya, a yayin da yake bayyana tasirin ƙasar ke dashi wajen wakiltar nahiyar Afika a hukumar.
Read Also:
Da yake jawabi a yayin wani taron tattaunawa mai taken “tasirin Afika” a taron duba tattalin arzikin duniya da aka yi a birnin Davos na kasar Sweden a ranar 21 ga watan Janairun 2025, ministan ya koka ga kwamitin sulhu ta MDD bisa rashin Afirka a cikin hukumar, yayin da yake bayyana cewa kusan kashi 60 cikin 100 na kudurorin majalisar sun shafi batutuwa masu alaka da Afirka.
Ya kuma yi nuni da cewa, da yawa daga cikin dokokin da Majalisar ta fitar na da illa ga nahiyar ta Afirka, ciki har da dokar sare dazuzzuka, wadda ta haramta sayen amfanin gona daga yankunan da aka sare dazuka, tare da yin watsi da kamfanonin fasaha da ke kera na’urorin da ke ba da damar sare dazuka a nahiyar.
Tuggar ya ƙara da cewa, ƙarƙashin mulkin shugaban Najeriya Bola Tinubu Kasar ta samu ingantuwar lamura kuma duniya ta shaida.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1463 days 19 hours 19 minutes 54 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 21 hours 1 minute 19 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com