Home General Najeriya ta buƙaci zama mamba a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya

Najeriya ta buƙaci zama mamba a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya

Najeriya ta bukatar kasancewar ta mamba a hukumar sulhu ta Majalisar Ɗinkin Duniya a yayi taron duba lamuran tattalin arziki na duniya wato DAVOS 2025 wanda ke gudana a Switzeland.

Ministan harkokin Najeriya Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ne ya nuna buƙatar ganin Najeriya ta kasance cikikkaiyar mamba ta hukumar sulhi ta Majalisa Ɗinkin Duniya, a yayin da yake bayyana tasirin ƙasar ke dashi wajen wakiltar nahiyar Afika a hukumar.

Da yake jawabi a yayin wani taron tattaunawa mai taken “tasirin Afika” a taron duba tattalin arzikin duniya da aka yi a birnin Davos na kasar Sweden a ranar 21 ga watan Janairun 2025, ministan ya koka ga  kwamitin sulhu ta MDD bisa rashin Afirka a cikin hukumar, yayin da yake bayyana cewa kusan kashi 60 cikin 100 na kudurorin majalisar sun shafi batutuwa masu alaka da Afirka.

Ya kuma yi nuni da cewa, da yawa daga cikin dokokin da Majalisar ta fitar na da illa ga nahiyar ta Afirka, ciki har da dokar sare dazuzzuka, wadda ta haramta sayen amfanin gona daga yankunan da aka sare dazuka, tare da yin watsi da kamfanonin fasaha da ke kera na’urorin da ke ba da damar sare dazuka a nahiyar.

Tuggar ya ƙara da cewa, ƙarƙashin mulkin shugaban Najeriya Bola Tinubu Kasar ta samu ingantuwar lamura kuma duniya ta shaida.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp