Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi kira ga rundunar ƴansandan Najeriya su dinga amfani da ƙwarewa, da kaucewa bayanan da ka iya tada hankali yayin gudanar da ayyukansu, musamman a jihar.h
Read Also:
Hakan na zuwa ne bayan damuwar da aka nuna kan sanarwar ‘yan sandan jihar Kano na yiwuwar za a kai harin ta’addanci a jajibaren bikin Mauludin da mabiya ɗarikar Tijjaniyya suke gudanarwa a duk shekara, da aka shirya yi a filin wasa na Sani Abacha da ke jihar.
Kwankwaso ya bayyana hakan a shafinsa na X, inda ya ƙara da taya mabiya ɗarikar Tijjaniyya da gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da Sarki Sanusi Lamido Sanusi II, kan nasarar yin taron Maulidin lami lafiya.
A makon da ya wuce ne dai, rundunar ‘yansandan jihar Kano ta fitar da sanarwar gargaɗi kan barazanar kai harin ta’addanci a jihar, da buƙatar a dakatar da bikin Maulidin da yake tara ɗaruruwan mutane daga sassan jihar da jihohi makofta.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1486 days 2 hours 51 minutes 5 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1468 days 4 hours 32 minutes 30 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com