Home General Bello Turji ya bayyana aniyar mika wuya – Manjo janar Christopher Musa

Bello Turji ya bayyana aniyar mika wuya – Manjo janar Christopher Musa

Babban Hafsan Sojojin Najeriya, Janar Christopher Musa a jiya Juma’a ya bayyana cewa fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji ya bayyana aniyar mika wuya. Ya bayyana hakan ne a lokacin da aka gayyace shi a cikinn wani shiri na gidan talabijen mai zaman kan sa a kasar.

Manjo Janar Christopher Musa, ya kara da cewa hare-haren da sojoji suka yi a baya-bayan nan, wanda ya kawar da wasu kwamandojin Turji da wasu mukarrabansa, ya karya logon shugaban ‘yan ta’addan.

Hakan ne ya tilasta masa sakin da dama daga cikin mutanen da ya yi  garkuwa da su, lamarin da ke nuni da shirinsa na ajiye makamai.

Yan ta’adda suna cikin al’umma; mutane sun san su. Don haka, wani lokacin idan sun gan su, kafin ka sami bayanin, kamar sa’o’i biyu ne – mutumin ya motsa. Don haka idan bayanin ya same ka, kafin ka matsa ya bar yankin.” Inji Janar Musa.

Ya kara da cewa, “Amma zan iya gaya muku, mun fitar da na biyu a matsayinsa, mun fitar da mafi yawan hakimansa, hasali ma ya tilastawa yanzu ya saki mafi yawan mutanen da ke karkashinsa.

Ina gaya muku kwanan nan ya fara cewa ba ya son komai, a shirye yake ya mika wuya.” Duk da cewa Turji ya bayyana aniyar mika wuya, Janar Musa ya jaddada muhimmancin daure masu aikata ta’addanci, musamman wadanda ke da alhakin mutuwar ‘yan kasa da ba su ji ba ba su gani ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp