Home General Bello Turji ya bayyana aniyar mika wuya – Manjo janar Christopher Musa

Bello Turji ya bayyana aniyar mika wuya – Manjo janar Christopher Musa

Babban Hafsan Sojojin Najeriya, Janar Christopher Musa a jiya Juma’a ya bayyana cewa fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji ya bayyana aniyar mika wuya. Ya bayyana hakan ne a lokacin da aka gayyace shi a cikinn wani shiri na gidan talabijen mai zaman kan sa a kasar.

Manjo Janar Christopher Musa, ya kara da cewa hare-haren da sojoji suka yi a baya-bayan nan, wanda ya kawar da wasu kwamandojin Turji da wasu mukarrabansa, ya karya logon shugaban ‘yan ta’addan.

Hakan ne ya tilasta masa sakin da dama daga cikin mutanen da ya yi  garkuwa da su, lamarin da ke nuni da shirinsa na ajiye makamai.

Yan ta’adda suna cikin al’umma; mutane sun san su. Don haka, wani lokacin idan sun gan su, kafin ka sami bayanin, kamar sa’o’i biyu ne – mutumin ya motsa. Don haka idan bayanin ya same ka, kafin ka matsa ya bar yankin.” Inji Janar Musa.

Ya kara da cewa, “Amma zan iya gaya muku, mun fitar da na biyu a matsayinsa, mun fitar da mafi yawan hakimansa, hasali ma ya tilastawa yanzu ya saki mafi yawan mutanen da ke karkashinsa.

Ina gaya muku kwanan nan ya fara cewa ba ya son komai, a shirye yake ya mika wuya.” Duk da cewa Turji ya bayyana aniyar mika wuya, Janar Musa ya jaddada muhimmancin daure masu aikata ta’addanci, musamman wadanda ke da alhakin mutuwar ‘yan kasa da ba su ji ba ba su gani ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp