Home General Kwankwaso ya caccaki ‘yansandan Kano kan barazanar kai hari

Kwankwaso ya caccaki ‘yansandan Kano kan barazanar kai hari

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi kira ga rundunar ƴansandan Najeriya su dinga amfani da ƙwarewa, da kaucewa bayanan da ka iya tada hankali yayin gudanar da ayyukansu, musamman a jihar.h

Hakan na zuwa ne bayan damuwar da aka nuna kan sanarwar ‘yan sandan jihar Kano na yiwuwar za a kai harin ta’addanci a jajibaren bikin Mauludin da mabiya ɗarikar Tijjaniyya suke gudanarwa a duk shekara, da aka shirya yi a filin wasa na Sani Abacha da ke jihar.

Kwankwaso ya bayyana hakan a shafinsa na X, inda ya ƙara da taya mabiya ɗarikar Tijjaniyya da gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da Sarki Sanusi Lamido Sanusi II, kan nasarar yin taron Maulidin lami lafiya.

A makon da ya wuce ne dai, rundunar ‘yansandan jihar Kano ta fitar da sanarwar gargaɗi kan barazanar kai harin ta’addanci a jihar, da buƙatar a dakatar da bikin Maulidin da yake tara ɗaruruwan mutane daga sassan jihar da jihohi makofta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp