Home General NAPTIP ta ceto mata 9 masu juna biyu da aka kulle a...

NAPTIP ta ceto mata 9 masu juna biyu da aka kulle a masana’antar jarirai

Hukumar dake yaƙi da safarar mutane ta Najeriya NAPTIP ta bayyana cewa ta samu nasarar ceto wasu mata guda 9 masu juna biyu a wani gidan da ake ajiye  matan domin su riƙa haihuwar yaran da ake sayarwa.

Jami’in yaɗa labarun hukumar ta NAPTIP Vincent Adekoye ne ya bayyana nasara da jami’ansu suka samu ga manema labaru a yayin da yake gabatar musu da jawabi.

Adekoye ya ƙara da cewa an sami wurin ne a cikin wani rukunin gidaje a yankin Ushafa dake ƙaramar hukumar Bwari dake Abuja babban birnin tarayyar ƙasar, a yayin da ya ke cewa sun mamayi wannan wuri ne bayan wasu bayanai da suka samu daga wasu masu kishin ƙasa.

Ya ce an samu waɗannan mutane ne a kulle a cikin wani gida a sanadiyar ɗaya daga cikin waɗanda suka killace matan da ba’a fayyace shi ba, bayan da aka ɗaukesu aikin na aika-aikar da suka nema ta  wani shafinsu na yanar gizo.

Adekoye ya kuma ce, Darakta-Janar ta Hukumar, Hajiya Binta Adamu-Bello, ta yabawa bangaren shari’a, bisa gagarumin hukuncin da aka yanke na yankewa wani Bishop Kenneth Duke hukunci.

An dai ce Duke ya yi wa wata yarinya ‘yar shekara 12 fyade, wacce diya ce ta ɗaya daga cikin mabiya cocinsa a Abuja.

Shugabar ta ce wannan hukuncin na iya zama izna ga ire-iren masu irin wannan aika-aikar, yayin da ta yi gargadin cewa hukumar ba za ta kyale duk wanda ya karya dokarta ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp