Home General NAPTIP ta ceto mata 9 masu juna biyu da aka kulle a...

NAPTIP ta ceto mata 9 masu juna biyu da aka kulle a masana’antar jarirai

Hukumar dake yaƙi da safarar mutane ta Najeriya NAPTIP ta bayyana cewa ta samu nasarar ceto wasu mata guda 9 masu juna biyu a wani gidan da ake ajiye  matan domin su riƙa haihuwar yaran da ake sayarwa.

Jami’in yaɗa labarun hukumar ta NAPTIP Vincent Adekoye ne ya bayyana nasara da jami’ansu suka samu ga manema labaru a yayin da yake gabatar musu da jawabi.

Adekoye ya ƙara da cewa an sami wurin ne a cikin wani rukunin gidaje a yankin Ushafa dake ƙaramar hukumar Bwari dake Abuja babban birnin tarayyar ƙasar, a yayin da ya ke cewa sun mamayi wannan wuri ne bayan wasu bayanai da suka samu daga wasu masu kishin ƙasa.

Ya ce an samu waɗannan mutane ne a kulle a cikin wani gida a sanadiyar ɗaya daga cikin waɗanda suka killace matan da ba’a fayyace shi ba, bayan da aka ɗaukesu aikin na aika-aikar da suka nema ta  wani shafinsu na yanar gizo.

Adekoye ya kuma ce, Darakta-Janar ta Hukumar, Hajiya Binta Adamu-Bello, ta yabawa bangaren shari’a, bisa gagarumin hukuncin da aka yanke na yankewa wani Bishop Kenneth Duke hukunci.

An dai ce Duke ya yi wa wata yarinya ‘yar shekara 12 fyade, wacce diya ce ta ɗaya daga cikin mabiya cocinsa a Abuja.

Shugabar ta ce wannan hukuncin na iya zama izna ga ire-iren masu irin wannan aika-aikar, yayin da ta yi gargadin cewa hukumar ba za ta kyale duk wanda ya karya dokarta ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp