Home General Martanin gwamnatin jihar Zamfara kan rahoton UNICEF na tamowa

Martanin gwamnatin jihar Zamfara kan rahoton UNICEF na tamowa

Zamfara

Hukumomi a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya sun mayar da martani game da bayanin da asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya ya yi cewa akwai yara dubu 250 da ke fama da matsananciyar yunwa daga cikin yara miliyan daya da dubu dari biyu da aka yi nazari a kansu a jihar.

Gwamnatin jihar ta ce lokacin da ta karbi mulkin jihar ta tarar da harkokin kula da lafiya ba kamar yadda ta yi tsammani ba, amma a cewar kwamishinan yada labaran jihar, Mahmud Muhammad Dantawasa sun dauki matakai dai-dai gwargwado.

“Yanzu haka gwamnati na gyara asibitocin matakin farko da suke a karkara guda 62 wadanda yawancinsu angama gyaransu kuma yanzu haka ana raba maganin tamowa a asibitin.”

Gwamnatin ta kuma yi kira ga iyayen yara da su riƙa zuwa wadannan asibitoci domin karɓar maganin tamowar kyauta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp