Home General Majalisar dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar ta dauki matakai kan...

Majalisar dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar ta dauki matakai kan Kangwaye dake jihar

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano dake arewa maso yammacin Nijeriya ta bukaci gwamnatin jihar da ta umarci masu kangwaye (filayen da ba’a gina ba ko tsofaffin gidajen da ba kowa a ciki) dasu gine ko kuma su sayar da su.

Wannan na zuwa ne bayan kudurin da Dan majalisa mai wakiltar Karamar hukumar Kiru Usman Abubakar Tasiu ya gabatarwa zauren majalisar.

Kiru ya ce yawancin kangwaye da gidajen da baa karasa ba a jihar sun zama wuraren lalata tarbiya da barazanar tsaro.

Da yake bada gudunmuwa akan kudurin dan majalisa mai wakiltar Karamar hukumar Madobi Sulaiman Mukhtar Ishaq ya ce ba iya kangwaye ba, hatta gidajen da aka gina na kwankwasiya da Amana city da Bandirawo sun zama barazanar tsaro da tarbiyyar al’ummar Kano.

Majalisar ta kafa kwamiti domin binciko mata lamuran kangwaye, inda zata mika shi ga gwamnatin Kano domin tabbatar da gyara a al’amarin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp