Sojoji Nijeriya na cigaba da farautar Bello Turji

Dakarun Operation Fansan Yamma tare da haɗin gwiwar jami’an tsaron farin kaya (DSS), sun ce sun ƙwace tarin makamai a karamar hukumar Kauran Namoda na jihar Zamfara.

Dakarun sun kai samamen ne bayan samun bayanan sirri kan masu safarar makamai daga Jamhuriyar Nijar zuwa Najeriya.

Wata sanarwa da jami’in yaɗa labaran rundunar Laftanar-Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, ya ce sun kaddamar da farmaki ranar 27 ga watan Janairun 2025, abin da ya kai ga ƙwato makaman kan hanyar Namoda zuwa Zurmi.

Ya ce waɗanda ake zargin sun tsere zuwa cikin daji tare da barin motarsu bayan artabu da sojoji.

Kanal Abubakar ya ce bayan bincike da suka yi a cikin motar, sun gano makamai da dama da suka haɗa da bindigar AK-47 guda tara da harsasai daban-daban.

A ɗaya gefen, dakarun sun ce suna cigaba da neman inda Bello Turji yake wanda ake nema ruwa a-jallo – wanda yake cigaba da tserewa sojoji ta hanyar guduwa daga maɓoya zuwa maɓoya.

Dakarun sun tabbatar da cewa suna aiki tukuru domin kama Turji domin mayar da zaman lafiya a al’ummomin da suka addaba da hare-hare.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 2 hours 22 minutes 57 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 4 hours 4 minutes 22 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com