Nijeriya ta sake ciwo bashi don samar da Lantarki

Najeriya ta karɓo rancen dala biliyan 1.1 daga bankin raya Afirka (AfDB) don samar da wutar lantarki ga mutane miliyan 5 daga yanzu zuwa ƙarshen shekarar 2026.

A cewar Bayo Onanuga, mai ba shugaban kasa shawara na musamman, Shugaba Bola Tinubu ya bayyana hakan a cikin jawabin da Adebayo Adelabu, ministan wutar lantarki, ya gabatar, a taron da aka kammala na kwanaki biyu na inganta ɓangaren makamashi na Afirka a Dar es. Salaam, babban birnin ƙasar Tanzania.

Tinubu ya kuma bayyana cewa za a yi amfani da dala miliyan 200 na AfDB domin samar da wutar lantarki ga mutane 500,000 a ƙarshen shekarar 2025.

“Wannan babban buri ne, amma za mu iya cimma shi tare,” in ji Tinubu.

“A matsayina na shugaban Najeriya, na himmatu wajen ba aiwatar da aikin samar da makamashi, kuma mun ba da babban fifiko.”

Ya ƙara da cewa “Kamar yadda muka sani, Afirka na da wadatar albarkatun makamashi, amma har yanzu miliyoyin ƴan nahiyar mu ba sa samun ingantaccen makamashi mai araha.”

Shugaba Tinubu kuma jinjinawa Ajay Banga, shugaban bankin duniya, da Akinwunmi Adesina na AfDB saboda hangen nesan su na kawo sauyi, wanda ya ce “zai haskaka da kuma karfafa Afirka.”

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 13 hours 3 minutes 18 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 14 hours 44 minutes 43 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com