Home General Gwamnatin jihar Kano ta Amince da kashe sama da biliyan 8 domin...

Gwamnatin jihar Kano ta Amince da kashe sama da biliyan 8 domin manyan ayyuka 15

Majalisar zartaswar jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ta amince da kashe Naira 8,199,635,732.07 domin gudanar da manyan ayyuka 15 a fadin jihar.

Wannan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar bayan tattaunawa a taron majalisar zartarwa karo na 24 da aka gudanar a gidan gwamnatin Kano ranar Laraba.

An ware naira 2,737,518,204.96 domin gina ajin karatu mai ajujuwa huɗu a fadin kananan hukumomin jihar 44.

Haka kuma majalisar ta amince da fitar da naira 2,311,388,177.70 domin sake aikin gina titin shataletalen gidan gwamnati zuwa titin Lodge Road, zuwa Race Course zuwa shataletalen otal ɗin Daula, tare da ƙarin ayyukan da suka shafi titin asibitin Nasarawa, titin Dawaki da kuma titin Lugard.

An ware Naira 1,870,814,360.10 domin gyaran babban ɗakin taro na Africa House da ayyukan tuntuɓa a gidan gwamnati.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp