Home General Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia

Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia

Mai lamba ta 6 a duniya Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia za ta buga da Denmark sakamakon rauni a kafarsa

Rauni ya tilasta Djokovic, mai shekaru 37, ficewa a wasan kusa da na karshe na gasar Australian Open da Alexander Zverev na Jamus a makon jiya saboda raunin da ya samu, inda magoya bayansa a Melbourne suka yi masa ihu.

Zakaran na Grand Slam na sau 24 ya saka hoton gwajin MRI da aka yi masa a kafarsa ta hagu a shafukan sada zumunta inda ya rubuta cewa ya saka wannan ne domin masana raunin ƴan wasa su gani domin tabbatar da yanayin da ya sa shi ya fice daga gasar.

Serbia, wacce za ta yi rashin Djokovic, za ta kara da Denmark a wasan share fage na zagayen farko, wanda za a fara ranar Juma’a 31 ga watan Janairu.

Kyaftin din Serbia Viktor Troicki ya ce sun samu rauni na rashin Novak, amma har yanzu suna da ƙwarin gwiwar samun nasara.

Denmark suna da babban dan wasa, wato Holger Rune, amma ‘yan wasansu ma suna da kyau kuma ya yi imani da tawagarsu.

Tawagar Serbia yanzu ta ƙunshi Miomir Kecmanovic, Hamad Mededovic, da Laslo Dere, da kuma ƙwararrun ƴan double ‘yan’uwan Sabanov, Matej da Ivan.

Haka kuma Serbia za ta kasance ba tare da Dusan Lajovic ba saboda rauni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp