Home General Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia

Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia

Mai lamba ta 6 a duniya Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia za ta buga da Denmark sakamakon rauni a kafarsa

Rauni ya tilasta Djokovic, mai shekaru 37, ficewa a wasan kusa da na karshe na gasar Australian Open da Alexander Zverev na Jamus a makon jiya saboda raunin da ya samu, inda magoya bayansa a Melbourne suka yi masa ihu.

Zakaran na Grand Slam na sau 24 ya saka hoton gwajin MRI da aka yi masa a kafarsa ta hagu a shafukan sada zumunta inda ya rubuta cewa ya saka wannan ne domin masana raunin ƴan wasa su gani domin tabbatar da yanayin da ya sa shi ya fice daga gasar.

Serbia, wacce za ta yi rashin Djokovic, za ta kara da Denmark a wasan share fage na zagayen farko, wanda za a fara ranar Juma’a 31 ga watan Janairu.

Kyaftin din Serbia Viktor Troicki ya ce sun samu rauni na rashin Novak, amma har yanzu suna da ƙwarin gwiwar samun nasara.

Denmark suna da babban dan wasa, wato Holger Rune, amma ‘yan wasansu ma suna da kyau kuma ya yi imani da tawagarsu.

Tawagar Serbia yanzu ta ƙunshi Miomir Kecmanovic, Hamad Mededovic, da Laslo Dere, da kuma ƙwararrun ƴan double ‘yan’uwan Sabanov, Matej da Ivan.

Haka kuma Serbia za ta kasance ba tare da Dusan Lajovic ba saboda rauni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp