Home General Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia

Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia

Mai lamba ta 6 a duniya Novak Djokovic ya fice daga gasar cin kofin Davis da Serbia za ta buga da Denmark sakamakon rauni a kafarsa

Rauni ya tilasta Djokovic, mai shekaru 37, ficewa a wasan kusa da na karshe na gasar Australian Open da Alexander Zverev na Jamus a makon jiya saboda raunin da ya samu, inda magoya bayansa a Melbourne suka yi masa ihu.

Zakaran na Grand Slam na sau 24 ya saka hoton gwajin MRI da aka yi masa a kafarsa ta hagu a shafukan sada zumunta inda ya rubuta cewa ya saka wannan ne domin masana raunin ƴan wasa su gani domin tabbatar da yanayin da ya sa shi ya fice daga gasar.

Serbia, wacce za ta yi rashin Djokovic, za ta kara da Denmark a wasan share fage na zagayen farko, wanda za a fara ranar Juma’a 31 ga watan Janairu.

Kyaftin din Serbia Viktor Troicki ya ce sun samu rauni na rashin Novak, amma har yanzu suna da ƙwarin gwiwar samun nasara.

Denmark suna da babban dan wasa, wato Holger Rune, amma ‘yan wasansu ma suna da kyau kuma ya yi imani da tawagarsu.

Tawagar Serbia yanzu ta ƙunshi Miomir Kecmanovic, Hamad Mededovic, da Laslo Dere, da kuma ƙwararrun ƴan double ‘yan’uwan Sabanov, Matej da Ivan.

Haka kuma Serbia za ta kasance ba tare da Dusan Lajovic ba saboda rauni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp