Gwamnatin Kano ta ce za ta fito da wasu da Sabbin hanyoyin tattara zakkah tare Kuma da rabawa mabukata yadda yakamata
Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka Lokacin kaddamar da shugabannin hukumomi biyu na Shari’a da na Zakkah a gidan Gwamnati.
Abba Kabir Yusuf ya ce Jihar Kano na da dimbin attajirai, to sai dai a bangare guda ta na fama da yawan almajirai da mabarata , Wanda ya bukaci hukumar Zakkah da KHubsi da ta fito da wasu hanyoyi na karba Zakkah daga wajen attajirai a wani yunkuri na rage yawan mabarata a JIhar kano.
Read Also:
Shugabannin hukumomin da Gwamnan ya kaddamar sun hada da Barrister Habibu Shekh Dan Almajiri a matsayin Shugaban hukumar Zakkah da Khubsi, sai Shekh Abbas Abubakar Daneji a matsayin Shugaban hukumar Shari’a.
Sauran wakilan hukumar sun hada da Shekh Malam Ali Dan Abba a matsayin kwamishina na biyu a hukumar shari’ah da Malam Abubakar madatai Mai Ashafa da sayyadi Nafi’u Umar Harazumi da Kuma alaramma Gwani Hadi Gwani Tahir
Wakilinmu na fadar Gwamnati ya ruwaito mana Gwamnan na Jan hankulan malaman da su yi amfani da gogewa da Ilimi wajen fito da Sabbin tsare tsare da za su kawo ci gaban addinin musulunci a Jihar.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1463 days 12 hours 8 minutes 49 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 13 hours 50 minutes 14 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com