Home General NLC ta dakatar da yin zanga-zanga Kan tsadar Data da kudin kira

NLC ta dakatar da yin zanga-zanga Kan tsadar Data da kudin kira

Kungiyar kwadago ta janye zanga Zangar da ta shirya gudanar wa a Talatar nan sakamakon Karin kudin kiran waya da na Data.

Wannan ya biyo bayan wata ganawa da ta yi da wakilan gwamnati a ofishin sakataren gwamnatin tarayya a daren Litinin, kungiyar kwadagon ta ce ta yanke shawarar dakatar da zanga-zangar har sai an dawo teburin tattaunawa.

Da yake zantawa da manema labarai bayan taron, shugaban kungiyar na kasa Joe Ajaero, ya ce gwamnati ta amince da kafa wani babban kwamiti da zai duba daukacin tsarin kudin Kiran waya.

A cewarsa, kwamitin zai kunshi wakilai biyar daga bangarorin biyu kuma ana sa ran zai mika rahoton bincikensa cikin makonni biyu.

Ya kara da cewa kungiyar za ta dauki matakan zanga-zanga da yajin aiki nan gaba, mutukar ba’a Sami wata matsaya ba kan rahoton Kwamitin .

Idan za,a iya tunawa dai a makonnin da Suka gabata ne hukumar Sadarwa ta kasa ta amincewa kamfanonin sadarwa masu zaman kanau da su kara kashi Hamsin na kudin Kiran waya da na amfani da data, wacce ta Kai ga kungiyar kwadago barazanar fita zanga zanga a ranar hudu ga watan Fabarairu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a Kano
X whatsapp