Home General NLC ta dakatar da yin zanga-zanga Kan tsadar Data da kudin kira

NLC ta dakatar da yin zanga-zanga Kan tsadar Data da kudin kira

Kungiyar kwadago ta janye zanga Zangar da ta shirya gudanar wa a Talatar nan sakamakon Karin kudin kiran waya da na Data.

Wannan ya biyo bayan wata ganawa da ta yi da wakilan gwamnati a ofishin sakataren gwamnatin tarayya a daren Litinin, kungiyar kwadagon ta ce ta yanke shawarar dakatar da zanga-zangar har sai an dawo teburin tattaunawa.

Da yake zantawa da manema labarai bayan taron, shugaban kungiyar na kasa Joe Ajaero, ya ce gwamnati ta amince da kafa wani babban kwamiti da zai duba daukacin tsarin kudin Kiran waya.

A cewarsa, kwamitin zai kunshi wakilai biyar daga bangarorin biyu kuma ana sa ran zai mika rahoton bincikensa cikin makonni biyu.

Ya kara da cewa kungiyar za ta dauki matakan zanga-zanga da yajin aiki nan gaba, mutukar ba’a Sami wata matsaya ba kan rahoton Kwamitin .

Idan za,a iya tunawa dai a makonnin da Suka gabata ne hukumar Sadarwa ta kasa ta amincewa kamfanonin sadarwa masu zaman kanau da su kara kashi Hamsin na kudin Kiran waya da na amfani da data, wacce ta Kai ga kungiyar kwadago barazanar fita zanga zanga a ranar hudu ga watan Fabarairu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp