Home General Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da...

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da zubar da shara a jihar

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin tarar kuɗi naira dubu 25 ga duk wanda aka samu da laifin tofar da yawu ko majina akan titunan birnin Kano.

Hakan ya biyo bayan dokar da majalisar ta amince da ita na tabbatar da tsaftar Muhalli ta cikin shirin ayyukan gyara birnin Kano da kawatashi domin samar da birni mai cike da tsafta a Najeriya.

Shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin Kano kuma dan majalisar Dala Hon. Lawan Husaini wanda ya yi wa manema labarai karin bayani, inda ya ce wajibi ne gwamnatin kano ta dauki matakan da suka dace wajen tsaftace birnin Kano, domin dawo da martabar birnin a idanun duniya.

Dan majalisar yace abin kunya ne da takaici yadda wasu ke yawan tofar da yawu ko face majina akan hanya duk lokacin da suka ga dama.

wakilin mu na zauren majalisar jihar kano ya ruwaito mana cewa majalisar tayi Karatu na biyu akan yiwa hukumar kwashe shara da tsaftar Muhalli garambawul.

Daga cikin gyaran dokar hukumar ta kwashe shara harda, bukatar samar da cikakken Mataimakin hukumar da kuma bata cikakkiyar dama ta aikinta yadda ya kamata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a Kano
X whatsapp