Home General Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da...

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da zubar da shara a jihar

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin tarar kuɗi naira dubu 25 ga duk wanda aka samu da laifin tofar da yawu ko majina akan titunan birnin Kano.

Hakan ya biyo bayan dokar da majalisar ta amince da ita na tabbatar da tsaftar Muhalli ta cikin shirin ayyukan gyara birnin Kano da kawatashi domin samar da birni mai cike da tsafta a Najeriya.

Shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin Kano kuma dan majalisar Dala Hon. Lawan Husaini wanda ya yi wa manema labarai karin bayani, inda ya ce wajibi ne gwamnatin kano ta dauki matakan da suka dace wajen tsaftace birnin Kano, domin dawo da martabar birnin a idanun duniya.

Dan majalisar yace abin kunya ne da takaici yadda wasu ke yawan tofar da yawu ko face majina akan hanya duk lokacin da suka ga dama.

wakilin mu na zauren majalisar jihar kano ya ruwaito mana cewa majalisar tayi Karatu na biyu akan yiwa hukumar kwashe shara da tsaftar Muhalli garambawul.

Daga cikin gyaran dokar hukumar ta kwashe shara harda, bukatar samar da cikakken Mataimakin hukumar da kuma bata cikakkiyar dama ta aikinta yadda ya kamata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp