Home General Bamu Fara daukan sabbin Ma’aikata ba- KAROTA

Bamu Fara daukan sabbin Ma’aikata ba- KAROTA

Hukumar Kula da Zirga- zirgar Ababen Hawa ta jihar Kano KAROTA ta musanta jita-jitar da ake yadawa na fara daukar aiki a Hukumar.

Shugaban Hukumar KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka a ranar lahadi, ta bakin mai magana da yawun Hukumar Nabilusi Abubakar Kofar Na’isa inda Yace Babu gaskiya a batun daukar Sabbin Ma’aikata.

Nabilusi Kofar Na’isa Ya ce Hukumar ta lura da jita-jitar da ake yadawa na fara daukar sabbin Jami’an Hukumar wadanda hakan ba gaskiya ba ne kwata-kwata.

Sai dai Kuma sanarwar tace Hukumar na tsaka da aikin tantance daukacin Jami’an KAROTA domin duba yuiwuwar daukar sabbi.

A don haka Hukumar ke gargadin jama’a, da su guji yada jita-jitar fara daukar sabbin Jami’an na Hukumar ta KAROTA

Hukumar ta ce duk wanda ta kama da hannu wajen yada jita-jitar zata dauki matakin sharia a kansa.

Engr. Faisal ya roki jama’a da su yi gaggawar sanar da Hukumar ta KAROTA ko ofishin ‘Yansanda mafi kusa wanda duk aka samu yana yada jita-jitar

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp