Home General Bamu Fara daukan sabbin Ma’aikata ba- KAROTA

Bamu Fara daukan sabbin Ma’aikata ba- KAROTA

Hukumar Kula da Zirga- zirgar Ababen Hawa ta jihar Kano KAROTA ta musanta jita-jitar da ake yadawa na fara daukar aiki a Hukumar.

Shugaban Hukumar KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka a ranar lahadi, ta bakin mai magana da yawun Hukumar Nabilusi Abubakar Kofar Na’isa inda Yace Babu gaskiya a batun daukar Sabbin Ma’aikata.

Nabilusi Kofar Na’isa Ya ce Hukumar ta lura da jita-jitar da ake yadawa na fara daukar sabbin Jami’an Hukumar wadanda hakan ba gaskiya ba ne kwata-kwata.

Sai dai Kuma sanarwar tace Hukumar na tsaka da aikin tantance daukacin Jami’an KAROTA domin duba yuiwuwar daukar sabbi.

A don haka Hukumar ke gargadin jama’a, da su guji yada jita-jitar fara daukar sabbin Jami’an na Hukumar ta KAROTA

Hukumar ta ce duk wanda ta kama da hannu wajen yada jita-jitar zata dauki matakin sharia a kansa.

Engr. Faisal ya roki jama’a da su yi gaggawar sanar da Hukumar ta KAROTA ko ofishin ‘Yansanda mafi kusa wanda duk aka samu yana yada jita-jitar

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp