Home General Yadda Sojojin Najeriya sun lalata wurare 12 da ake tace man fetur...

Yadda Sojojin Najeriya sun lalata wurare 12 da ake tace man fetur ba bisa ƙa’ida ba

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta lallata wurare 12 da ake tace man fetur ba bisa ƙa’ida a yankin Naija Delta da ke kudancin ƙasar.

Cikin wata sanarwar da muƙaddashin daraktan yaɗa labaran runduna ta 6 ta sojin Najeriya da ke birnin Fatakwal, Laftanar Kanal Jonah Danjuma ya fitar ranar Lahadi, ya ce dakarun sun kuma ƙwato lita 70,000 na man fetur, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Sojojin sun ce a wani farmakin mako guda da suka ƙaddamar tare da haɗin gwiwar sauran jami’ar tsaro sun samu nasarar lalata ƙananan jiragen ruwa shida da ƙwato bututun mai tara da aka sace, tare da kama mutum 16 da suke zargi da hannu a jihohin yankin huɗu.

Sanarwar sojojin ta kara da cewa dakarun sun ƙaddamar da farmakin ne tun daga ranar 27 ga watan Janairu zuwa 2 ga watan Fabarirun 2025.

Yankin Naija Delta ya yi ƙaurin suna da ayyukan ɓata-gari, waɗanda ke fasa bututun man fetur tare da sace man, wani abu da masana ke bayyanawa da yi wa tattalin arziin ƙasa zagon ƙasa.

Man fetur shi ne kan gaba a hanyoyin da Najeriya ke samun kuɗaɗen da gwamnati ke samu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp