Home General Yadda Sojojin Najeriya sun lalata wurare 12 da ake tace man fetur...

Yadda Sojojin Najeriya sun lalata wurare 12 da ake tace man fetur ba bisa ƙa’ida ba

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta lallata wurare 12 da ake tace man fetur ba bisa ƙa’ida a yankin Naija Delta da ke kudancin ƙasar.

Cikin wata sanarwar da muƙaddashin daraktan yaɗa labaran runduna ta 6 ta sojin Najeriya da ke birnin Fatakwal, Laftanar Kanal Jonah Danjuma ya fitar ranar Lahadi, ya ce dakarun sun kuma ƙwato lita 70,000 na man fetur, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Sojojin sun ce a wani farmakin mako guda da suka ƙaddamar tare da haɗin gwiwar sauran jami’ar tsaro sun samu nasarar lalata ƙananan jiragen ruwa shida da ƙwato bututun mai tara da aka sace, tare da kama mutum 16 da suke zargi da hannu a jihohin yankin huɗu.

Sanarwar sojojin ta kara da cewa dakarun sun ƙaddamar da farmakin ne tun daga ranar 27 ga watan Janairu zuwa 2 ga watan Fabarirun 2025.

Yankin Naija Delta ya yi ƙaurin suna da ayyukan ɓata-gari, waɗanda ke fasa bututun man fetur tare da sace man, wani abu da masana ke bayyanawa da yi wa tattalin arziin ƙasa zagon ƙasa.

Man fetur shi ne kan gaba a hanyoyin da Najeriya ke samun kuɗaɗen da gwamnati ke samu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp